KUNDIN KADDARATA BY HUGUMA

KUNDIN KADDARATA CHAPTER 42 BY HUGUMA

     Gefansa ta zauna cikin rashin jin dadi,tana jin kamar ta raba yaran da mamansu ne,ta dubi lukman
“Ya kamata zuwa gobe kaje ka dawo da mamarsu islam,kada a ja abun yayi nisa don Allah,yaran na buqatar mamarsu” kai ya kada baison gaya mata wani abu da zai daga mata hankali,a yanzun da karima ta dan tura ta bar gidan sai yake jin kamar an zare masa wata qaya data tsaya masa a maqoshi
“To naji” kawai ya fada.

     Kwana biyu tana masa mitar yaje ya dawo da karima arana ta uku yace kada ta sake masa maganar baiso,idan lokacin dawowa yayi zata dawo,ai ta saba ba yau farau ba,hakan ya sanya ta tsuke bakinta,hankalinta ya dan kwanta ganin yaran basu tada hankali sosai kan rashin dawowar mamansu ba.

       Cikin kwanakin da suka biyo bayan tafiyar karima baki daya gidan yayi dadi,kada ma lukman hajiya da nuwaira suji labari,da fari sumayya ta fara fuskantar matsala daga yaran saboda qarancin tarbiyya da suke da ita,amma sai ta jure tayi amfani da hikima irin tata,a hankali ta fara janye qananan,nuratu basma da syyada,islam ce kawai ta taqi biyuya,ta soma kwaso halin uwarta tsaf,hakan yasa ta tattarata ta watsar gefe,zasu hadu suci abinci tare,suyi karatu,ta basu labarai na annabawa da sahabbai,suna bala’in so ta basu tarihi,har rigima suke idan tace ta gaji,sosai ta shiga jikin yaran suka soma shaquwa da ita,ta koya musu abubuwa da dama wadanda ya kamata ace sun iya amma basu iya ba,kamar alwala,sallah,sallama idan zasu shiga guri,addu’ar sanya kanya,addu’ar bacci da tashi daga bacci,addu’ar shiga bandaki data fitowa,addu’ar fita daga gida da ta shigowa da yin bismillah da hamdala kafin da bayan gama cin abinci,su kansu yaran dadi sukeji,nuwaira tafi kowa murna takance
“Anty dama tuntuni kema ‘yar gidan nan ce,ai da tuni nayi saukar qur’ani ko?” Dariya takanyi tace
“To ai yanzun ba gashi na zo ba?,kuma zakiyi ne in sha Allah”,tarbiyya take basu sosai mai wuyar bari ko mantawa,tana musu ne bilhaqqi fisabilillahi,don har ga Allah tana son yaran,ko ba komai babansu da kakarsu na gwada mata qauna.

      A hankali sai itama islam din ta fara biyuwa,ta shige cikinsu,idan kaga sumayya da yaran zakayi zaton qannenta ne,dama gata gwanar son yara,abun ya yiwa hajiya dadi,wani lokaci har takan tsinci kanta da addu’ar kada Allah yasa karima dawo,don ita kanta yanzu anan bangaren take wuni sai dare zata kwashi jikokinta suje su kwana tare da ita a can,a yanzu sumayya ta koya musu qaunarta da ganin girmanta,ta bangaren lukman kansa yana mamakin yadda hankalinsa yake a kwance,sau tari ma sai ya mance da wata karima,kwanciyar hankali da nutsuwa ya samu sosai irin wadda bai taba samun irinta ba tunda ya fara aure,ba shakka sumayya ta dabance,zai kuma yi fatan kasancewa da ita har qarshen rayuwarsa,hatta da mai gadi da mai aikin gidan sunga sauyi,sun kuma ga banbanci,suma sun samu ‘yanci.

       Kwanci tashi har aka kusa shafe wata biyu ba motsin karima,sam sun mance ma basa maganarta,banda yaran da wani lokaci zasu dan tada zancanta shikenan an wuce gun,ta maida qaunar dake tsakaninsu baki daya saboda haka nuwaira ta samu matsayinta na babba a gidan,a yanzu takan iya tsawatarwa dukkaninsu sabanin daa da bata isa ba,basma ma na iya dungurinta ta wuce,da tace musu abu babu kyau zasu daina saboda ta gaya musu wanda keyin abinda babu kyau Allah zai sashi a wuta,ta wassafa musu yadda wuta take dai dai da tunaninsu yadda zasu gane haka ma aljanna,don haka da tace abu da kyau tofa zasu shiga yi saboda sun san aljanna sun san wuta.

1 2 3 4 5 6 7Next page

Related Articles

Back to top button

You cannot copy content of this page

Adblock Detected

YOU ARE USING ADBLOCK TURN IT OFF TO COUNTIUE BROWSING OUR WEBSITE