BA SONTA NAKE BA TAUSAYI NE

BA SONTA NAKE BA TAUSAYINE CHAPTER 16

Bayan taci abinci ta ɗan kwanta abin ka da jikin talaka tuni bacci yayi awon gaba da ita sama-sama cikin baccin ta taji tashin maganganu masu kama da faɗa acikin tsakar gidan nasu muryar hadiza ce ke tashi tana cewa.
“Kaga malam baka isa kazo ka sakani agaba nida yarana ba ita matar so ka barta da auren ka aka tana fita tun safe bata dawowa se dare ai baka taɓa bita kanta ba duk abin duniyar data ke shigowa dashi bata baka takai yaranta makaranta suna ɗaga mana kai, seni daka raina zaka saka agaba ɗan cinikin danai ka rance idan na hana ka hauni da cin zarafi wallahi wannan mutuwar zuciya ta wasu mazan hausawan tana cutar su”
Tashi hassana tayi tsam daga kwanciyar ta zauna sosai ta fara jin maganar malam shi kuma.
“Ke hadiza dakata ke har kina da bakin cemin mai matacciyar zuciya kin manta da taimaka miki nayi na aureki sabida kurmantar ki babu mai zuwa wajanki seni dana ɗauki lalura, Kuma hassana da kike maganarta ai nagaya mata cewa itace uban yanzu nina zare hannuna akan ta ita da yaranta ayi dai mugani in ruwan ido ze dafa shinkafa”
Yafaɗa cikin ɗaga murya.
“Ahayye! shagali to ai bari kaji da namiji irin ka malam gwara zawarci kai to meye marabarka da gawa agidan nan mai kake mana maika tsinana mana ka kashe zuciyarka a banza kaiba musaki ba,ko ita hassanar da kake tutuya kabar mata yaranta ai ba wata uwar kake tsinana musu ba yara da ran ubansu amman suna yawo kamar marayu sabida mutuwar zuciyar mahaifin su……..
Tas!!!
Ya wanke hadiza da mari hannunsa yana rawa yake ce mata.
“Ki fita a idanuna hadiza in kika ƙara magana sena sake ki! kuma bazan baki ƴaƴanki ba suyi bara tunda ubansu mai mutuwar zuciya ne”
Yafaɗi haka kuma ya tsugunna ya kwashe ƴan canjinta tas yayi ficewar sa tukubar mai tsire.
Zaman ƴan bori hadiza tayi a tsakar gidan tana rusa kuka!
Ƴaƴanta da suke laɓe a ɗaki suka fito suka cicciɓeta sukai ɗaki da ita.
Abin duniya duk yayiwa hadiza yawa gaba ɗaya komai ya fice mata akanta ga jarabar babansu basira ga takaicin sauyin da hassana ta samu a kwana biyu.
Duk abin da sukai hassana tana jinsu bata ko tanka ba, bare ta fito har wajan tara yaranta suka dawo daga makaranta abinci ta zuba musu suka ci tana tambayarsu wuninsu har sukai bacci.

1 2 3 4 5 6 7 8Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Related Articles

Back to top button

You cannot copy content of this page

Adblock Detected

YOU ARE USING ADBLOCK TURN IT OFF TO COUNTIUE BROWSING OUR WEBSITE