GIDAN AURE by ZAHRATEEY

GIDAN AURE CHAPTER 2 ZAHRATEEY

GIDAN AURE COMPLETE 

Www.bankinhausanovels.com.ng 

Sunana Mardiyya ni yar garin Kaduna ce mazaunan Lagos. A lokacin muna Lagos kafin mu dawo Kaduna da zama muna zaune ne a Getto Area, anguwa ne wanda ya tara yan iska da dama baga mazan ba baga matan ba. A lokacin kaf cikin anguwar babu gidan masu kudi sai gidan mu saboda muna da Generator sannan gidan mu nada feshin fenti wanda yake karawa gini kyau alhali kaf cikin unguwar babu irinsa. Ana mana lakabi da yan gayu ko kuma idan an gammu sai a rinka nuna mu ana cewa “iyakar gayu Annan” wato mun kure gayu iya gayu. Ni nice auta a gidan mu kuma karama a tsakanin yayyina, ina jss3 akayi bikin yayata wacce nake bi a lokacin shekaruna goma sha hudu, sai ya rage ni kadai ce a gidan.

Inada kawaye na hudu duk yan Kaduna kuma cikin ikon Allah sai duk mukayi aure a Kaduna, sai dai iyayena ne kawai suka koma Kaduna da zama nasu iyayen suna zaune a Lagos basu da alamun tashi su koma mahaifarsu.

Babban kawata wacce nafi kusanci da ita fiye da kowa itace Faiza, sai Nafi sai Jawahir sannan Zaliha. Faiza da Zaliha gidansu yana kallon gidan mu, sai Nafi gidansu na gefen gidan mu ta dama sai Jawahir ita kuma gidansu na gefen gidan mu ta hagu.

Dukan mu kawaye ne sosai makaranta ne kawai ya rabamu inda su suke makarantar gobnati ni kuma nake na private, islamiya kam tare muke zuwa mahaifina ke daukan dawainiyar mu, a haka har muka sauke alqurani me girma muka fara hadda. A lokacin Zaliha ta biyewa saurayi har ya mata ciki, kafinnan ma Mahaifiyarta tayi cikin shege da auren ta wanda hakan shine silar mutuwar auren ta, sai yayarta itama tayi cikin shege na uku inda sauran biyun suke 6arewa amma na ukun sai suka haifeshi tare da uwarta. Wato maman Zaliha kenan, a lokacin duk sai iyayen mu suka mana katanga da Zaliha muamalar mu da ita ba wani sosai bane ya mafi yawa a islamiya.

Bayan an gama da cikin shegen mamanta da yar uwarta sai kuma gata itama ta kunso nata, a lokacin duk mun gama sakandiri muna jiran sakamakon zuwa jamia. Bayan ta haihu sai iyayen saurayin suka musu aure saboda karamci irin nasu, kasancewar yana aiki a Kaduna sai suka tattara suka tafi, shekaru biyu tsakani akayi bikin Jawahir da Nafi suma duk aka kai su Kaduna, inda Jawahir ta auri dan abokin babanta ita kuma Nafi ta auri dan yayan babanta wanda matarsa ta rasu ta bar yara mata biyu. Kasancewar sun fara karatu a nan sai  babana ya nema musu transfer suka koma can da karatu, sai ya rage nida Faiza, mukam sai da muka gama jamia sannan mukayi aure inda Faiza ta auri wani dan makocinsu a Kaduna ni kuma na Auri wani Soja wanda muka hadu dashi a bikin yaye dalibai na makarantarmu.

1 2 3 4 5 6Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

You cannot copy content of this page

Adblock Detected

YOU ARE USING ADBLOCK TURN IT OFF TO COUNTIUE BROWSING OUR WEBSITE