HEEDAYA CHAPTER 50 BY By Khaleesat Haiydar
HEEDAYA CHAPTER 50 BY By Khaleesat Haiydar
Mumy ce xaune dakinta tana ma Shuraim wani kallon tace “Kai me yasa baka da mutunci ne Aliyu?” Da mamaki
yace “But Mum how do u expect me to know what happened bayan nace maki ni bana wajen, ni ban san me ya faru
ba, ki tambayi Abba” Wani kallo ta dinga yi masa, Bayan few minutes jin ta ki cewa komai yace “Kiran kenan
Mumy?” Ta jefa masa wani kallo ta nuna masa kujera tace “Xauna mu yi magana” Ba musu ya tafi ya xauna saman kujeran, tana kallonsa tayi kasa da murya tace “Aliyu ka gaya min tsakanin ka da Allah, ni dai nice na haifeka ba
wani ba….” Shi dai Shuraim kallonta kawai yake, tace “Tell me, do you have any feeling for Heedayah?” Kallonta ya
dinga yi da surprise, can yace “Wacece haka?” Tace “Auuu Heedayar ce baka sani ba?” Yace “Heedayah??” Ta hade
girar sama da ta kasa, can yace “Ohh, Wai Heedayah guda dai da na sani? Feeling na me kenan?” Ganin sai
hararansa take ya d’an yi murmushi yace “Idan ina da feeling for her xaki yrda wani tarayya ya hadani da ita ne?”
Tace “Why not? Ba ubanka bane yyi wahala da ita da rainonta? Ina ce a gidan nan ta taso? kuma ae nasan irin rainon
da aka yi mata ba wanda xai cutar da kai ko ni bane ko da wata alaka ta shiga tsakaninku” Shuraim yace “I don’t
have the feeling you are thinking Mum, ba gobe naji Abba yace xa a kai kudinta ba, Allah ya sanya alkhairi” Kasa ce
masa komai tayi, but she look shocked, ya mike yace “Allah ya tashe mu lfya” Daga haka ya nufi kofa as if babu
abinda ya damesa a lkcn, sai bayan da ya fita dakin nata ya kulle kofa ya ji kamar an axa masa abu me nauyi saman
kirjinsa, xaunawa yyi a hankali saman kujeran parlonta na few minutes, kafin ya mike da kyar ya fice daga parlon
gaba daya ya koma dakinsa. Washegari da safe Shuraim na kwance jin wayarsa dake vibrating a gefensa ya bude ido
a hankali ya jawo wayar yana kallon screen din, Number Mami ya gani, ya kalli wayar for few seconds snn ya daga