ZUMA BY SHATUUU

ZUMA CHAPTER 13 BY SHATUUU

ZUMA CHAPTER 13 BY SHATUUU

Www.bankinhausanovels.com.ng 

Na nufi wajen Daddy inata sakawa da kuncewa, Ina Kara weighing abinda na yanke, naje har kofar parlon se kuma na juya zuwa daki da sauri Ina girgiza kaina, is it a good decision I’m making? Ina Zama ummu tazo tace naje Daddy yana Kirana, hakan na Mike na fito zuwa parlon shi, gabana yana ta faduwa na wuce zuwa dakin nashi completely lost in thought. Yana tsaye yana gyara links din hannun shi, ya kalleni ya ganni kamar a birkice nake, yace

” Take it easy Mana, zauna”

Zama nayi jikina har rawa yakeyi, ya lura se ya miko min ruwan cikin tumbler yace

” Nanah meye ne matsalarki, ni nace kiyi deciding kuma ko meye decision din ki Zan saka Miki albarka”

Se naji na Dan nutsu, na gyara zaman nace

” Daddy Zan aura Abbah Prof”4

Na lumshe idanuna Ina adduar Allah yasa akan hanya nake, Allah yasa banyi zabin da zanyi da na sani ba. Wani murmushi Daddy ya sakar min yace

” Blessed you child! Ashe kina da hankali, Ina Miki fatan alkhairi a rayuwar ki,Ina fata zabin ki zai kaiki ga alkhairi. Kinyi tunani me kyau. Kije  ki ce mishi Ina son ganin shi da daddare yau dinnan!”

Se naji sanyi cikin Raina, na Mike jikina da kwari na nufi daki Ina jin farin ciki da cikar burin zuciyata. Da farko zuciyata na ingiza ni na karba Aliyu Amma ko kadan bayan nayi magana da hibba se naji mind dina duka sun canja, mindset Dina ya koma kan Abbah, bansan me yasa da nake kokarin zabar Aliyu ba, sede na kan kafa hujja da wannan na daya daga cikin hudubobin shedan lokacin da zakai abin kirki, musamman ma aure.

Ina na zaune sega kira da number dana goge dazun, hannuna nasa na dauka , kafin na gaishe shi yace min

” Why are you sorry?”

Nayi shiru Ina tunanin abinda Zan fada masa, se na tuna sakon Daddy

” Daddy yace ka sameshi da daddare”

Tabbas idan har zai dawamma da wannan farin cikin daya nuna min saboda zan zauna dashi inaga da tuni na kware shi kenan!

” Are you serious Amour? Bazaki gane irin farin cikin da nake ciki ba, Amma inshallah Zan nuna Miki shi a zahiri”

Nayi murmushi na jin dadin abinda yace, nace

” Then I’ll continue to make you happy forever!”

Nayi tunanin Yara ne kawai suke good in wordings se naga Shima ba baya ba, dukkan words din bakin shi are soothing, kalamai ne masu sanyi da sanyaya zuciya!

” Menene burin da kike son na cika Miki kafin na aureki?”

Nayi dan Jim sannan nace

“Burina naje wajen mummy kafin nayi aure sannan kuma na ganta a gurin bikina”

” Consider it done Amour!”

Da daddare wajen takwas Suka bayyana a gidan mu, Daddy yace ya bawa Abbah Prof aurena, ya yanke wata biyu kacal saboda yasan Abbah bazai so yayi ta jele gurina da girmana shi ba. Abbah ya gode ma Daddy tareda Masa alkawarin ranar monday zaa kawo kudin aurena da sadaki na. Cikin girma da mutunci aka gama komai, har zasu tafi Abbah ya dubi Daddy yace

“Daddy Ina Neman wata alfarma”

Daddy yace

” Prof menene?”

Yace

” Ina son na kai Fatima Niger idan ka yarda”

Daddy yace

STORY CONTINUES BELOW

” Why not! Babban dalilin hana Fatima zuwa gurin Aisha saboda Fatima Tasha wahala, nafi son duk ranar da zata je taje Mata complete human, nasan nayi kuskure sosae a rayuwata,da zaa dawo da lokaci Dana gyara. Nayi alkawarin se ta samu miji ta gama karatu sannan zata je. Duk lokacin daka shirya se ku wuce”

Abbah yayi mishi godiya sosae sannan Suka tafi, Babu Wanda ya fada min abinda ke faruwa, washegari Monday Abbah Suka kaso kudin nema Dana sadaki, Daddy ya kirani ya bani a hannu yace

” Na bada auren ki, Ina fata wannan zabin naki ya dawammar Miki farin ciki har karshen rayuwar ki”

Kasakasa na amsa Amin sannan na aje Zan fita,wayar Daddy ta fara ringing na Mika masa jin ya ambaci

” Tana asibiti? To zata taho yanzun! Allah ya sauketa lafiya!”

Ya aje wayar yace min

” Amina na labor, Salem yace ko Zaki je?”

Kaina na gyada Ina jin anxiety yana kamani, Kaya na dauka ban fadawa sauran ba na tafi driver Dan zasu iya cewa zasu bini, a general ya kaita Ina shiga matron din na zuwa, Dan dama tace masa duk lokacin da matar shi zata haihu ita zata karba Dan uwar dakin shi ce. Tare muka zauna bayan na shiga naga ba yadda take duk jikina yayi sanyi, wajen karfe daya na dare ta haihu, ta samu baby boy. Ni aka fara bawa bayan matron ta goge shi tas, na saka Masa Kaya na rungume shi Ina jin tsantsar kaunar shi, tamkar Salem yayi kaki ya tofar. Se asuba na fara fadawa mutane, Abbah Prof ya fara Kirana Dan tunanin shi Ina gida

” Amour voice din ki kamar baki bacci ba”

Na danyi dariya Ina jin dadin yadda yake fahimtar duk yanayin danake ciki, nace

” Tun eleven Ina asibiti Amina ce ta haihu”

” Shi ne baki fada min ba, Allah ya Raya me aka samu?”

” Ina bada hakuri, naga it’s late May be kana gida shiyasa. It’s a baby boy”

Ya mishi addua tareda ce min whenever nayi tunanin yana gida I should text him, sannan yace kafin yaje office zai leko mu. Da mukai sallah na fara Kiran Yan uwa Ina fada musu, Yaya Rahma dake a gari a asuban ta karaso muka hadu muka gama komai, Nawwara da Amal Suka tafi gidan Amina Dan kintsawa kafin mu dawo, Daddy wajen six yazo, a waje aka saka masa kujera ya zauna sannan Salem ya kawo mishi yaron ya Masa huduba, Salem yace

” Daddy kayi Masa huduba da Ibrahim”

Munji dadin karar da yayi Mana, aka rada Masa Ibrahim na saka masa Abid. Se na tuna ai baban Salem ma sunan shi Ibrahim, yaro yaci suna biyu kenan. Yan ward dinsu Wanda suke night da Wanda Suka fito morning duk sunxo. Wajen seven Abbah ya karaso, ni na taho dashi daga inda sukai parking,

” Baki ya kasa rufuwa anyi da”

Na Kara sakin murmushi nace

” Ba zaka gane ba”

1 2 3 4 5 6Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Related Articles

Check Also
Close
Back to top button

You cannot copy content of this page

Adblock Detected

YOU ARE USING ADBLOCK TURN IT OFF TO COUNTIUE BROWSING OUR WEBSITE