HEEDAYA CHAPTER 28 BY By Khaleesat Haiydar
HEEDAYA CHAPTER 28 BY By Khaleesat Haiydar
Kallon Zainab Heedayah tayi, Zainab tace “Ko shi ne?” Heedayah ta dinga kallon motar, can tace “Aa ba da motar
nan nake ganinsa ba” Zainab tace “To ki je ki duba” Karasawa Heedayah tayi gun motar, taga an sauke Windshield
din motar, sosai gabanta ya fadi bayan sun yi ido hudu da shi, sanye yake da wandon sojoji da polon su, ya dauke kai
daga kallonta ya kara haska ma Zainab fitila, Kamar ana tilasta Heedayah tayi kasa da murya tace “Ina yini” bata jira
ya amsa ba ta bar wajen tana turo baki, Zainab sai kallonta take har ta iso, Heedayah tace “Ke ake kira” Zainab ta
xaro ido tace “Ni kuma? Waye ke kirana?” Heedayah tace “Oho ki je ki gani” karasawa Zainab tayi tana d’ari d’ari, Shuraim ya sakar mata murmushi, ta buda ido sosai ganinsa tace “Lahh ashe ya Shuraim ne, kai ma dinner din ka
xo?” Ya hade rai yace “Dinner kuma? No, not at all” tace “To me kaxo yi nan?” Yace “Yanxu xan wuce wajen aiki,
na ajiye wasu ne” Zainab tace “Ohk Ina yini Ya Shuraim” yace “Lafiya lau, me yasa ita kadai ta xo gun motar sbda
taga anyi flash din fitila maimakon ku biyu?” Zainab tace “Ohh ni ce nace taje ta ga wa ke haska mu” Yace “Wato ita
ce fitsararriya, da wani ne haka xata xo ta tsaya masa a mota tana kallonsa ko?” Zainab tace “Aa fa Yaya, ni nayi
insisting taje ta ga waye da gaske” kallonta ya tsaya yi, can yace “Then… Don’t do that again, Ina Farida?” Zainab
tace “Sun shiga ciki” yace “Ke ina pass din naku?” Zainab tace “Gashi a jaka, nata na wajenta” yace “Ohk, till after
the dinner kar ku fito waje” Zainab tace “Dama ai baxa mu fito ba Yaya” Yace “Good” tace “Yanxu xaka wuce?”
Yace “Ehh” tace “Toh Allah ya kiyaye” Heedayah dai na can tsaye nesa da su sai turo baki tayi, can kuma sai ta tabe
bakin, wani abu kamar kwandala taga ya gangaro inda take, ta dinga kallon d’an abun me shige da ring da ya kwanta