HEEDAYA CHAPTER 26 BY By Khaleesat Haiydar
HEEDAYA CHAPTER 26 BY By Khaleesat Haiydar
Rungume kaka Heedayah tayi ta kankameta cike da murnan ganinta, rabonta da kaka tun da suka yi hutun jss3 third
term, sae da kaka ta kare mata kallo daga sama har kasa sannan ta turata tace “Aa ni ki rufa min asiri kar ki cuceni ki
kada ni kasa ana bikin jikokina, ki bar ganin kin tsayince kamar falwaya, nima ina yan mata haka nake duk da dai
yanxun ma ni ba guntuwa bace” Mami tayi dariya ta xauna tace “Sannu kaka….” kaka tace “Yanxu Rakiya
fisabilillahi auren ‘ya yan Umaru fa ake kika ki xuwa sai yau, ke da ya kamata ace tun ana sauran sati daya xaki
tattaro kayanki ki dawo nan, xumunci fa ba abun wasa bane ba abun yadawa bane, idan ma ke baxa ki xo ba ai sai ki
turo mana Heedayah tunda ta mu ce, ki bar ganin an sakar maki ita ki xata galaba kika ci a kanmu, ni ce nan nake ta
tausan Amadu amma kiris ya rage ya kwace ‘yar sa tunda ba ke kika tsinto masa ita ba, Kuma ba ke kika warkar
mata da idonta ba” Ba yabo ba fallasa Mami tace “Toh sai yah xo…. ina jiransa” A hankali Heedayah ta xamo kasa
tace “Ina kwana kaka?” Ko kallonta Kaka bata yi ba tace “Ina da labarin sun yi hutu yau kusan sati biyu amma kin ki
barin ta xo ta gaisheni ta gaida wan Amadu sannan ta tafi gidan shi Amadun ta gaishesa idan ya kama har kwana
biyu tayi, wannan dai ba yi bane, fitina a kwance take dai idan kika tada ta ke kika sani… Ko jiya sai da Amadu yace
xai je ya dauketa nace ban ki ta tasa ba amma yyi hakuri muyi bikinmu mu cashe lafiya, bayan biki sai yaje can ku ci
kanku bbu ruwan wani, wllh tllh haka aka yi ki tambayi wnn yaro Shureen ai tare suka shigo jiyan” Shuraim dai na
tsaye dakin yana danna wayarsa, Mami taki cewa komai, Shuraim ya gaida Mami, ta amsa da murmushi tana
tambayarsa ya aiki, Farida dake danna wayarta ita ma tace masa “Ina yini” yace “Lafiya lau” Murya can kasa
Heedayah tace “Ina yini” ya ci gaba da danna wayarsa bai ce komai ba, kaka tace “To dai wnn shine dalilin ma da na
kira ki nace na ji ku shiru, Amadu ne ya xo nan xai daga mana hankali wai xai je amso yarinya, ni dai na samu na
lallabasa ya wuce, wnn yarinya dai ya fi kowa iko a kanta kema kin sani sai dai idan kina da karancin tsoron Allah,
don haka ki raba kanki da fitina ki daina kokarin rabata kwata kwata da uban rikonta ba wani ya tsinto masa ita ba,
jifa jifa sai ki turata da wnn yarinya Farida su je suyi kwana biyu gidansa haka ake yi ba ki yi bake bake a kan
yarinya ba ke kadai, da bai tsintota tana galantoyi ba a ina xa ki santa Rakiya? to ga dai akwatina nan, daya
matsiyacin mijin kwara biyar ya kawo gasu can a gantale ko budewa jama’ah bana yi, dayan kuma d’an albarka guda
takwas da uban kaya a wani jakar ya kawo… Ku yi ta dubawa tunda na yadda da ke baxa ki cuce mu ba, kinsan
akwai masu sace kaya idan sun xo gani, yanxu dai kasuwa wnn yaran xa su rakani, in je in siyo masu mafici,
matankadi, gwa-gwa, maburgi, ludayan miya, ‘yar kwalla karama me ado, turmi da kwarya, duk gantalallun iyayen
basu siya masu ba basu san shi aka kai mana lkcn mu ba auren yyi albarka da izinin Allah, wai su ‘yan xamani to ba
dani xa ayi wnn lalacewar ba, xan tafi yanxu da kai na in siyo masu a bakin dogo, nace wnn mutumi Shureen ya kai
ni a mota ya ki, da yake tunda ya samu sojan nan ya fara saka ilifon dinsu yake ganin kowa bbu gashi, ynxu kafin ku
shigo sae kinga fitsaran da yyi min, to sojan karya ma da bai isa rike bindiga ba har ynxu, uban wa xai basa bindiga
dama, ni dai har yau ban gansa da bindigan wasan yara ba balle na gasken amma har shine xai dinga raina ma
mutane wayo” Ta gefen ido Shuraim ya ke kallonta, Mami dae sai murmushi take ta ki cewa komai, Heedayah ta
taba jakarta da sauri jin kamar vibration, mikewa tayi ta shige bandaki, Shuraim ya bi ta da kallo har ta rufe kofa, Jin