HEEDAYA COMPLETE BY By Khaleesat Haiydar

HEEDAYA CHAPTER 3 BY By Khaleesat Haiydar

 HEEDAYA CHAPTER 3 BY By Khaleesat Haiydar


                 Www.bankinhausanovels.com.ng 

Jin budewar gate ya sa Alhaji Ahmad ya mike ya isa jikin tagar dakinsa yana kallon compound din gidan don ganin 

wanda xai fita, motar yayansa ne ya shigo compound din, ya bi motar da kallo har yyi parking, sannan ya girgixa kai 

ya koma ya xauna… Ba a dau lkci ba kuma wayarsa ya fara ring, ya duba ganin yayan nasa ke kiransa ya mike ya 

fita dakin, kwance ya ga Heedayah ta fara bacci nan kasa, ya d’aga ta ya kwantar kan kujera sannan ya fita, direct 

main parlor ya wuce, ya tadda wansa Alhaji Umar zaune saman kujera ga Hajiya Maryam xaune parlon ta sha kunu 

kai kace bata ta6a dariya ba, xaunawa yyi ya gaida Yayan nasa, Alhaji Umar ya amsa yana kallon Hajiya Maryam 

yace “Me ke faruwa Maryam” Ta kwantar da murya tace “kana ji Alhaji, Ko awa daya ba ayi ba da dawowan 

barrister daga kano, amma sai me??” Nan ta kwashe komai ta tsara masa, tana matsar kwalla tace “Saninta muka yi 

Alhaji? Ko me muka hada da wannan yarinyar? Mun san me yasa iyayen suka jefar da ita da har shi xai daukota, to 

gaskiya naga abun ba wanda hankali xai dauka bane shi sa na kira ka don kayi intervene don gaskiya I don’t know 

what came over Barrister, ban san me ya samesa ba, kawai muna xaman xaman mu ya ja mana magana….” Alhaji 

Umar na kallon kanin nasa yace “Barrister wace yarinya ce wannan ka dauko ka kawo cikin gidan ka?” Alhaji 

Ahmad ya jinginar da kansa da kujera yace “Doctor nasan da kai ka ga yarinyar nn xaka yi fiye da abinda nayi ma… 

Sincerely I mean no harm to my family, taimako kawai nayi sbda Allah, and I thought they will also welcome the 

idea, na xata xa su so taimakon da nayi….” da sauri Hajiya Maryam ta katse sa tace “To family dinka basa son 

taimakon nan gaskiya, ur idea isn’t welcome, kawai ka maida ta inda ka ganta, idan kuma xuciyar ka baxai yarda ka 

maida ta ba to ka kai ta gidan marayu…” Wani kallo ya jefa mata yace “Baki isa ki bani order a gidana ba Maryam, I 

did what I know is right, you are not in the place to kick away my decision, nace baki isa ba” Alhaji Umar na 

kallonsa yace “Hold on bawan Allah, bana son hayaniya, ka saurareni….” Alhaji Ahmad yace “Dr if you are in 

anyway doubting me ka kira abokin ka Asp Usman, he will explain everything to you, Babu abinda xai boye maka, 

shi ma ya bani go ahead din tahowa da yarinyar when I request doing so, ban taho da yarinyar nan ba sai da izini da 

sa hannun Asp….” Mikewa Alhaji Umar yyi bayan shirun wani lkci yace “Ynxu ina yarinyar take?” Barrister ya 

mike yace “Mu je ka ganta tana sama parlona” Bin bayansu Hajiya Maryam ma tayi xuwa part din mai gidan nata da 

1 2 3 4 5 6 7Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Related Articles

Back to top button

You cannot copy content of this page

Adblock Detected

YOU ARE USING ADBLOCK TURN IT OFF TO COUNTIUE BROWSING OUR WEBSITE