HEEDAYA CHAPTER 3 BY By Khaleesat Haiydar
HEEDAYA CHAPTER 3 BY By Khaleesat Haiydar
Www.bankinhausanovels.com.ng
Jin budewar gate ya sa Alhaji Ahmad ya mike ya isa jikin tagar dakinsa yana kallon compound din gidan don ganin
wanda xai fita, motar yayansa ne ya shigo compound din, ya bi motar da kallo har yyi parking, sannan ya girgixa kai
ya koma ya xauna… Ba a dau lkci ba kuma wayarsa ya fara ring, ya duba ganin yayan nasa ke kiransa ya mike ya
fita dakin, kwance ya ga Heedayah ta fara bacci nan kasa, ya d’aga ta ya kwantar kan kujera sannan ya fita, direct
main parlor ya wuce, ya tadda wansa Alhaji Umar zaune saman kujera ga Hajiya Maryam xaune parlon ta sha kunu
kai kace bata ta6a dariya ba, xaunawa yyi ya gaida Yayan nasa, Alhaji Umar ya amsa yana kallon Hajiya Maryam
yace “Me ke faruwa Maryam” Ta kwantar da murya tace “kana ji Alhaji, Ko awa daya ba ayi ba da dawowan
barrister daga kano, amma sai me??” Nan ta kwashe komai ta tsara masa, tana matsar kwalla tace “Saninta muka yi
Alhaji? Ko me muka hada da wannan yarinyar? Mun san me yasa iyayen suka jefar da ita da har shi xai daukota, to
gaskiya naga abun ba wanda hankali xai dauka bane shi sa na kira ka don kayi intervene don gaskiya I don’t know
what came over Barrister, ban san me ya samesa ba, kawai muna xaman xaman mu ya ja mana magana….” Alhaji
Umar na kallon kanin nasa yace “Barrister wace yarinya ce wannan ka dauko ka kawo cikin gidan ka?” Alhaji
Ahmad ya jinginar da kansa da kujera yace “Doctor nasan da kai ka ga yarinyar nn xaka yi fiye da abinda nayi ma…
Sincerely I mean no harm to my family, taimako kawai nayi sbda Allah, and I thought they will also welcome the
idea, na xata xa su so taimakon da nayi….” da sauri Hajiya Maryam ta katse sa tace “To family dinka basa son
taimakon nan gaskiya, ur idea isn’t welcome, kawai ka maida ta inda ka ganta, idan kuma xuciyar ka baxai yarda ka
maida ta ba to ka kai ta gidan marayu…” Wani kallo ya jefa mata yace “Baki isa ki bani order a gidana ba Maryam, I
did what I know is right, you are not in the place to kick away my decision, nace baki isa ba” Alhaji Umar na
kallonsa yace “Hold on bawan Allah, bana son hayaniya, ka saurareni….” Alhaji Ahmad yace “Dr if you are in
anyway doubting me ka kira abokin ka Asp Usman, he will explain everything to you, Babu abinda xai boye maka,
shi ma ya bani go ahead din tahowa da yarinyar when I request doing so, ban taho da yarinyar nan ba sai da izini da
sa hannun Asp….” Mikewa Alhaji Umar yyi bayan shirun wani lkci yace “Ynxu ina yarinyar take?” Barrister ya
mike yace “Mu je ka ganta tana sama parlona” Bin bayansu Hajiya Maryam ma tayi xuwa part din mai gidan nata da