YAR LEKEN ASIRI COMPLETE BY ANUP JANYAU

YAR LEKEN ASIRI CHAPTER 6 BY ANUP JANYAU (_SPY_🎥)

YAR LEKEN ASIRI CHAPTER 6 BY ANUP JANYAU

(_SPY_🎥)

                Www.bankinhausanovels.com.ng 

Wani irin taku Kuzeem keyi tamkar wata zakanya, cike da tsagwaron jarumta wacce batada algus. Yayinda Meerah ke gefenta sai Security’s da ke bayansu, har suka iso bak’in wani k’aton building, wanda a nan ne office d’in L.G Aliyu Iko yake.  Cikin sauri Security’s d’in wurin suka bud’e mata k’ofa tare da sadda kawunansu a k’asa saboda jin nauyin rashin bata girman da suka saba yi. D’an guntun murmushi Kuzeem tayi sannan ta shige ciki, ta bar su Meerah tsaye a wurin, don basuda izinin shiga ciki. Daidai lokacin wani Security ya iso wurin tare da shaida musu ana son ganinsu ga baki d’aya, hakan yasa suka bar wurin su dukansu.

Ba shiri Major Khalil yayi saurin dakatar da dariyar da yake yi, yana mai sake tariyo ma k’wak’walwarsa yanayin kallon da Kuzeem tayi masa kafin ta bar office d’in. Hannayensa biyu ya hard’e a k’irji, tare da jinjina kai yace;

“Tabbas akwai tarin ma’anoni a cikin kallon da tayi min, tou me hakan ke nufi?. Menene dalilin da yasa aka koresu a hukumar nan?, wanne irin laifi ne suka aikata?, kuma meyasa ba’a zauna da ni a cikin meeting d’in da akayi ba?, wanda k’a’ida ne duk sanda za’a zauna meeting irin haka da ni ake zama, amma sai gashi wannan karon ba’a neme ni ba. Ba ko shakka akwai lauje cikin nad’i, don haka ya zama dole in binciko ainahin bakin zaren”.

Yana gama fad’in haka ya bar office d’in da sauri kamar zai tashi sama, yana fitowa harabar hukumar ya hango Security’s jere cikin layukka sun k’ame wuri d’aya, hannayensu a goshinsu alamar Salute, yayinda B.G Atiku Tanko ke tsaye a gabansu fuskar nan tashi a turnuk’e babu alamar rahma, tamkar bai tab’a dariya ba.

Tsaye yayi tare da rik’e k’ugu yana kallon yanda Security’s d’in suka daza layukka, sai kuma ya d’auke kansa ya mayar gefe kana ya sake maida dubonsa a garesu, da wani irin sauri ya sake kallon gefe, karaf idanuwansa suka sauka kan su Kuzeem da ke nufosa ita da Bilal.  Kallonsu kawai yake yi yana son nazartar yanayin da suke ciki amma ya kasa tantance ainahin yanayinsu, har suka iso ta wurin da yake tare da wuce sa, da kallo ya bi bayansu yana k’iyasta abubuwa da dama a ransa, yayinda su ko kallon banza bai ishesu ba.  Kai tsaye wurin Security’s d’in suka nufa, ko wannensu fuskarsa ba yabo ba fallasa, daidai lokacin mutane hud’un da zasuyi aiki tare suka iso wurin suma, hakan yasa suka jera a tare, kallo d’aya zakayi musu kasan an had’a zaratan jarumai masu jini a jika, wad’anda ke tsoratar da tsoro da kansa, k’i gudu sa gudu.

Wannan jerawar da sukayi ba k’aramin birge sauran jami’an sukayi ba, wad’anda ko wannensu tun d’azun sai tambayar kansa yake laifin me wad’annan manyan jigunan hukumar sukayi aka koresu?, saidai sun kasa samun amsar tambayar, yayinda wasu sukayi farin ciki da hakan, wasu kuma suka shiga jimamin lamarin. Suna isowa wurin suka tsaya bayan B.G Atiku Tanko, hakan yasa Security’s d’in suka shiga sauke hannayensu k’asa a tare, cikin wani irin salo mai birgewa, saidai kallo d’aya zaka yima yanayin fuskokin wasu daga cikinsu kasan sam basu tare da walwalarsu.  

Juyowa B.G Atiku Tanko yayi wurin su Kuzeem yana yimusu wani irin kallo wanda suka dad’e da fahimtar ma’anarsa, sannan ya maida dubonsa ga Security’s d’in da ke jere a gabansa, cikin wata irin murya mai amo da sauti yace;

“Jami’ai!!!”.

“Yallab’ai!!!”.

Muryarsu ta k’arade wurin.

“A juya sashen dama”.

B.G  Atiku Tanko ya sake fad’a musu da k’arfi cike da bada umurni.  Cikin sauri suka buga k’afafuwansu na hagu a k’asa, tare da yimasa Salute sannan suka juya b’angaren dama. Idan kaga yanda sukayi abun sai yayi matuk’ar birgeka. Sake tamke fuska yayi sannan ya juyo ya kalli su Kuzeem ba tare da ya furta komai ba yayi musu alama da hannu a kan su tafi.  A tare sukayi mishi murmushi sannan suka juya tare da barin wurin suka nufi inda sukayi perking motocinsu. Babu wanda ya sake furta komai daga cikinsu kowa ya shiga motarshi, aka bud’e musu get suka bar wurin.

 

Wani irin iska Major Khalil ya furzar daga bakinsa don ga baki d’aya kansa ya k’ulle ya kasa hasaso komai, ya kasa gano bakin zaren, cikin sauri ya nufi hanyar zuwa upstairs, k’ofar na bud’ewa ya shiga, elavotor ya shiga tare da danna 3rd floor, yana tsayawa ya fito ya nufi bakin wata k’ofa da aka rubutama *DGN(Director General) Colonel Mansur Iliyas Sani*.  Hankali tashe ya murd’a handle d’in k’ofar, ya fad’o cikin tamfatsetsen office d’in mai girman gaske da tsaruwa.

Saurin d’agowa wani babban mutum dake zaune cikin office yana danna sytem d’in gabansa yayi tare da kallonsa, sannan yace;

“Taya akayi ka san na dawo?”.

Da sauri Major Khalil ya iso wurinshi tare da jan kujera ya zauna, sannan yace;

“Wallahi Uncle  bansan ka dawo ba kawai hasashen zuciyata ne”.

Kai ya gyad’a yace;

“Me ke tafe da kai?”.

“Wata tambaya nake da ita wacce na san kai kad’ai ne zaka iya bani amsarta”.

Hannu Colonel Mansur Iliyas ya kai ya cire glass d’in idonshi, sannan ya rufe sytem d’in gabanshi yace;

“Ina jinka”.

1 2 3 4 5 6Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

You cannot copy content of this page

Adblock Detected

YOU ARE USING ADBLOCK TURN IT OFF TO COUNTIUE BROWSING OUR WEBSITE