ZUMUNTAR KENAN BOOK 3 COMPLETE by Sumayyah Abdul-kadir

ZUMUNTAR KENAN BOOK 3 CHAPTER 8 by Sumayyah Abdul-kadir

ZUMUNTAR KENAN BOOK 3 CHAPTER 8  by Sumayyah Abdul-kadir

                  Www.bankinhausanovels.com.ng 

iyaye da ‘yan uwana. 

Daga uwata har ubana kowa fushi yake dani, Walida kadai ke kula ni a gidan, haka nan kullum Baba zai fita sai ya ce. 

“Tunda haka kike so, wato ga dakin uwarki ga naki, inta wuce dakina ki bita da ido kina kissime-kissime ai sai kiyi ta zama”. 

Wannan magana ba karamin kona min rai take yi ba, tun ina kuka har na saba. A zuciyata kuwa Allah Ya isa ga Fa’iz tafi dubu biyar. 

Na rame, na fige, na zama ‘yar firit dama jikin ba wani jiki ba. Nayi niyyar komawa Giwa amma na kasa saboda kurarin da nayi a baya cewa ba zan sake zuwa gidan Hajjah ba. Wuri daya ne nake tunanin idan naje zanji sanyi, wato wurin Maman Kaduna, to amma in ina da kunya ai bana dosheta ba alhalin kiyayyar danta na neman zauta ni. Ko babu komi ranar da Fa’izun ya ga damar dawowa me na isa nayi mishi akan idon uwarsa? Gara dai ya kwaso jiki ya kawo namu gidan. 

Haka Zanirah da Aliyu suka yo min waya wai hakuri suke bani abinda suka yi min ranar bikinmu a Giwa su wasa ne suke min. Tsaki nayi na kife wayar nayi tagumi da hannu bibbiyu. 

Bayan kwana biyu kuma, sai Ummi da Bashir suma suka bugo, amma su ba hakurin suke bani ba, korafi suke wai naki inje inga gidansu, to inzo in raka Ummi awo tana da ciki dan sati biyu. 

Na ce, “Sai ku bari ya cika wata daya tukunna mu fara zuwa awo, kunji ko ‘yan abu kazan uba marassa kunya”. 

Ummi ta ce, “Da fatan (this very big) ashar (is for 

—_= 

me alone not with my husband) don mu albarkar miji muke nema ba ma zaginsa””. 

1 2 3 4 5 6Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Related Articles

Back to top button

You cannot copy content of this page

Adblock Detected

YOU ARE USING ADBLOCK TURN IT OFF TO COUNTIUE BROWSING OUR WEBSITE