. Sultana ba ita ta farka ba sai tsakiyar dare , wara! ido tafara yi , ahankali take bud’e idon harta bud’e gaba d’aya , tabbas yanzu ta sake yarda batada gata ita Sultana yau har namiji ya ci galba akan ta bayan shine sanadin rabata da gatan ta gaskiya ya cuceta, ahankali hawaye yake sauk’a akan fiskan tah , lokaci d’aya kuma ta sake sakin k’ara! saboda tsananin ciwon da taji maranta nayi , haka taringa juyi agun babu mai taimakon ta , duk ta fita haiyacin ta ta had’a gumi saboda azaba, haka ta kwana tanacin bak’ar wahala takuma yanke hukuncin barin gidan sa , gara taje tanemi gafara wajen mahaifin ta tasan zai tausaya mata tunda yana sonta abunda ya mata ma yayi ne saboda 6acin rai badan ransa yana sobah…..+
Malam Habu duniya ta samu , yanzu kam ya zama mutun sosai , idan ba wanda ya sanshi sosai ba baza kace shine wannan wahalalle da yayi fama da jinyan bah , yanzu ya samu lafiya ga kuma kula da yake samu agun sirikin sa bana wasa bah, dan k’aton kanti ya bud’e mar bayan gida da ya siyamar , tunda yace shi bayason zaman birni.
Ya kuma samu mata sun daidai ta kansu har ya aura , tunda zama bbu mata bai tace bah a gunsa matsayinsa na babbah , dan yanzu saki uku ne tsaka ninsa da Lantana.
Kuluwa kam Allah ya kar6i abunsa tun bayan cikin da tayi , sunje birni da saurayin akan za a cire cikin , anan doctor d’in ya cire abunda za sumar amfani a jikin ta ya fito ya shaidawa saurayin nata cewa Kulawa ta rasu , Jamilu ko a jikin be damu bah , saima cewa da yayi ya futa da masifa yanzu zai samu ya sake , amma sai ya nunawa doctor din cewa ya damu da mutuwan tah har yana shirin fita a haiyacin sah, cewa doctor din yayi zai samo mota ya dawo doctor yace bbu damuwa, Jamilu yana barin gu ya gudu ya koma k’auye ba tare da ya bawa wani labari bah.
Doctor ganin shiru yayi yawa Jamilu bai dawo ba , yasa shi fara zulumi dan daman ana yawan zargin asibitin nasa wai ana kashe mutane kasan cewan private neh .
Ganin har an kwana an wuni shiru yasa shi yin waya akazo aka sayi sauran gangan jikin ma , dan ya fahinci Jamilu guduwa yayi .
Acan k’auye bbu wanda ya nemi Kuluwa , kasan cewan ta kanyi kwana ki bata gida , tana gun samarin .
Sannan ko da tana gidan ma bawai tana iya taimakon uwar bane duk da laluran da Allah ya jarrabeta.
Shi kam Malam Habu daman ya jima da ya fesu , daga ita har uwar tah kunga kenan bbu mai neman Kuluwa tayi mutuwan asara ko mai mata addu’ah bbu…
A 6angaren Lantana zuwa yanzu tana samun sauk’i bbu laifi , ta kuma ga darasi a cikin rayuwa ta shiga hankalin ta , saidai ta fara damuwa da rashin Kuluwa na tsawon lokaci bata zo gidan bah , tun tana maganan har tagaji tayi shiru, sauk’in da ta fara samu yasa dole ta fara fita bara domin neman abunda zata ci , tunda ko ta zauna bbu mai bata , rayuwa kenan shiysa shuka alkairi ma yana da rana Allah yasa mu dace.
Daddy kam da Mom Faty duniya ta samu , yawon bud’e ido suke yi sosai , yau suna wannan wannan k’asar gobe suna wancan tankar wasu k’ana nan yara.
Hakan ya bawa Mom Faty daman juya daddy kamar wani waina tare da kwashe duk wani abunda ya mallaka , tunda yana mugun tsoron ta sharrin asiri yana da yawa , haka kuma zuwa yanzu an mantar dashi Sultana Sam, bashi da wani tunani da ya wuce na zainab d’iyar Momy Faty , gashi yanzu ko waya basa yi duk abunya damesu saka makon wayoyin su da aka kwashe sunja wani shago siyayyah suna ta faman love har aka kwashe basu ankara ba , hakan yasa dole suka sanja layi kawai , gashi basu sa ranan dawowa bah ace warsu ai zainab tana hanu mai kyau basu da matsala sunsan tana samun kulawa…
Gari na wayewa a daddafe Sultana ta shirya tabar gidan ,duk da ciwon da yake damun ta ga kuma jini da yake binta dak’er take tafita , saida tayi tayi tafiya mai tsayi kafin tasamu abun hawa kasan cewan safiya ne sosai ga kuma yanayin garin hadiri, koma ba haka ba damn abun hawan na wuya agun tunda anguwan manya ne mota ne kawai suke yawo agun…
Sultana ce tsaye tana ta faman dukan get d’in shiga gidan su , amma shiru ba a bud’e bah , gashi ruwa ya sauk’a harya fara dukan ta , can dai bugun yayi yawa wani k’aton mutun ne ya fito a gidan fiskan nan a had’e bbu annuri yana ta fuci kaman wani zaki .
Sultana cikin tsiwa tace “kai kuma waye ?”, Kakemin tanbaya haka kaman wani ubana.
“Ban sani bah , ya bata amsa.
Tsaki Sultana taja!, Sannan taci gaba da surfamar bala’i dan Sam ta manta da matsalar ta da kuma ciwon da take ji .
Mutumin tsayuwa kawai yayi yana kallon ta tare da tinanin irin matakin da zai dauka akan tah .
Sultana ganin ya mata banza kuma ruwa na dukan ta tasa ta bin gefen sa zata wuce , finciko ta yayi da k’arfi tare da shak’e wuyan ta duk idonta sun fito waje , sake ta yayi dak’ar fi ta bugu da get kamar zata fad’i ga ruwa yana k’ara karfi , wani k’aran azaba Sultana ta saki dan ciwon ya dawo mata sabo , agun ta zube ta fara juyi .
Mutumin ganin haka yace ta tashi tabar gidan karta mutumar , ganin bata da niyyan tashi yasa shi d’aga ta ya fitar waje sannan ya dawo ya rufe k’ofa yayi wucewan sa ciki .
Sultana ta jima tana juyi agun sannan ta mik’e dak’er ta nufi wata runfa ta tsaya , sai faman 6ari takeyi lokaci d’aya kuma zazzabi mai tsana ni ya rufe tah…..
…….. Sultana waje ta samu ta zauna ta nata faman 6ari!, ga idon ta da yayi jah hawaye na zuba!, hak’oran ta sai faman rawa suke , takurewa tayi agu d’aya tana ta faman sak’e sak’e a cikin ranta , tanbanyan kanta take yi to shin waye wannan me hanata shiga gidan abun nata ?” Me hakan yake nufi , tanbaya sosai take ma kanta saidai bbu amsa .+
Lokaci d’aya garin yayi duhu k’arfin ruwa ya k’aru sosai , ga tsawa da walk’ira da akeyi akai akai .
Mik’ewa Sultana tayi jiki na 6ari! sai faman matsan k’walla take yi , wani gidan kusa dasu ta nufa nocking ta shiga yi , ta jima tana bugawa kafin mai gadin ya fito ya bud’e k’ofan.
Malam Nuhu na ganin Sultana ya gane fiskan bazai ta6a mantawa da cin mutuncin da tamar ba , k’aramar yarinya kamar Sultana ta d’aga hannu ta shara mar maruka, Allah bazai barta ba.
Rok’on da Sultana ta kemar tana kuka!, shi ya dawo da Malam Nuhu daga dogon tinanin da ya tafi, “please ka taimaka min zai shiga gidan na fake ta fad’a jiki na 6ari hak’on ranta na fama rawa!.
Wani mugun kallo ya watsa mata , alamun jin haushi “zaki 6ace a nan ko sai na watsa miki mari?” , harkin mata cin mutun cin da kika min?” , Wlhy baza ki shiga bah .
Magiya Sultana take mar amma ya k’i sauraron ta, hanun sa ta kamo “dan Allah ka taimaka min…
A fusace! Malam Nuhu ya d’auke Sultana da mari!, “kinsan Allah idan kika sake gigin ta 6ani sai na miki illah kaji ja’irar yarinya , kin manta marin da kika ta6a min?”….
Rass! zuciyan Sultana ya tsinke , tabbas ta tina marin da tamar, wata rana tafito za taje gun wani party, tana sauri har ta buge Malam Nuhu da mota , fitowa tayi a fusace ta d’auke sa da mari har sau uku , ba ta kuma bi ta kansa ba bare ta duba ko yaji ciwo ta wuce tabar gun..
Malam Nuhu yaji zafin abun amma dole ya hak’ura tunda shi talaka ne bai da wani gata , abokin sa mai gadi shine ya bashi shawaran yakai k’aran yarinyan wajen uban ta , amma ko da yaje sai Alhaji Musa ya bashi rashin gaskiya harda fad’a Wai ana shiga rayuwan Sultana da yawa suna son kashe tane, Sultana da wowa tayi daga duniyar tinanin da ta fad’a , mik’ewa tayi tana tafiya cikin ruwan tana kuka!.
Wani ne ya bita da gudu kasan cewan be santa ba shi , ya mata magana dan bak’one a unguwan.
“Baiwar Allah wa kike nema be?”.
STORY CONTINUES BELOW

Sultana cikin kuka! ta amsa mar da “gidan mu nazo saidai wani ya hanan shiga ya ce gidan sane , nazo daya gidan kuma na samu na fake shine mai gadi ya mare ni, ya hanan shiga , ta kai k’arshen maganan tana matsar kwalla bakin ta na 6ari.
“Aw wancan gidan kike fad’a wai?”
Kai ta d’agamar alaman shi.
“Ai me gidan ya siyar da gida ya tashi , wasu ne suka dawo gidan…
“What , me kace?”
“Na ce masu gidan sun tashi wasu ne suka dawo gidan.
“Ohk Dan Allah ko kasan gidan da suka koma?.
A’a , kar nayi k’arya bansani bah.
“Ohk na gode , ta fad’a tana ci gaba da tafiya.
“Kinga na ce ba, ko zaki fake anan zuwa ruwan ya tsaya?”.
“No kar ka damu, na gode, ta fad’a tana ci gaba da tafiya.
Kai tsaye gidan su Sultan ta wuce, saidai iya kacin ta haraban gidan , bata samu shiga ciki ba ance mata suna bacci, saidai ta jira sai sun tashi , bayan da ta iya dole ta zauna kusa da d’akin mai gadi tad’an fake tana jiran sanda zasu tashi.
Ruwa bashi ya tsaya ba har 10:am , ba a d’au wani lokaci bah Abban Sultan ya fito rik’e da key d’in mota a hanun sa, sai matar sa wato Hajiya Sadiya mahaifiyar Sultan, kana ganin ta kasan tana cikin farin ciki saboda yanda take ta faman fara’a!, Sam hankalin su beje gun da Sultana ke ra ka6e bah , Sultana ganin yana shirin shiga mota ya sata saurin mik’ewa daga in da take ta nufi gun motan sai faman rawan sanyi take yi , kana ganin ta kasa marar lafiya , jikin motan taje taja ta tsaya tana duban su kafin tayi magana, Ummyn Sultan ne, ta daka mata tsawa “keh! Lafiya me ya kawo ki gidan nan?”.
Abba ne ya juya sa sauri yana duban inda matar tasa take kallo Sultana ya gani kamar a mafarki, baki bud’e ya fara tanbayan ta , “Keh lafiya ?”.
Shiru Sultana ba amsa.
Magana Abba ya sake yi a karo na biyu , ” ba magana nake miki ba , nace me yake faruwa ?”.
Ummy ne ta dubeta tare da daka mata tsawa , “keh! ba magana a ke miki bah?” , Ko bakya jine?”.
“I hate , rainin wayoo, ta k’arisa maganan tana dokawa Sultana kallo banza me cike da k’yama.
Dak’er Sultana ta iya bu6e baki tace”Abba gun ku nazo….
“Gunsa dai amma banda ni wlhy, ta na kaiwa nan tabar gun , dan ta masifan tsanan yarinyan gani take kamar ita ce silan lalacewar D’an ta Sultan.
Abban duban Sultana yayi cikin tausayawa yace” maza muje ciki kimin bayani meyake faruwa.
Bbu musu Sultana ta bishi suka shiga falo, bbu kowa a ciki , waje Sultana ta samu zauna ,Abba waya ya d’auka ya kira matar sa bbu yanda ta iya dole ta fito falon , Sultana ya kalla sannan ya ce “muna sauraron ki me yake tafe sake?”.
Sultana cikin kuka ta fara bashi labarin duk abunda yake faruwa , da sakin da Sultan ya mata da duk abunda ya faru sai dai Sam Abba be san cikin jikin ta na layi bane.
Sosai ran Abba ya 6aci, waya ya d’auka yayi kiran Sultan cikin 6acin rai yake magana akan yazo yana son ganin sa , Hajiya Sadiya taji dadin hakan sosai.
“Toh ni banga wani amfanin Kiran yaron nan ba , me zaka mar?” , Shi mafa mutun ne mai yanci gaskiya bazan dau walak’anci ba , ta koma gidan ubanta man tunda tana dashi, cikin shege wlhy bazamu kar6a bah tadai nemi Wanda ya mata , kuma tunda ya sake ta ai shikenan me kuma ya saura a tsakanin mu?”.
Tsawa Abba ya dakawa Ummy akan ta fure mar baki , baya son shirme bbu yanda ta iya dole tayi shiruu.
Ba’a d’au lokaci ba Sultan ya iso gidan , falon ya shigo shima ya samu gu ya zauna , gaishe da Abba ya fara yi saidai Sam yak’i amsa wa , Ummy ya gaisar ta amsa .
Abba ne ya fara magana kamar haka, ” dan ubanka me ka aikata kenan ?” , Haka kaga anayi a gidn ku ?”, Matar ka ta sunna kake cewa tayi cikin shege?” To ina ta samo sa ?” Waya mata?….
Shiru Sultan bbu magana .
Abba ne ya sake daka mar tsawa!, “ba da kai nake magana bah?”.
“Abba wlhy ni bnmata ciki ba , banma taba shiga dakin taba bbu abunda ya shiga tsakanin mu , dam! k’irjin Abba ya buga.
Amma sai ya dake yace” me kake nufi?”.
Charab Ummy ta kar6i zancen “me ya ke nufi kuwa , yace ba cikin sa bane ko dole sai ya kar6a?”, Wlhy d’ana yana da tarbiya Sam bazai yiwu bah…
Abba kansa ya bala’in kullewa , Sultana ya duba sannan ya ce”keh zaki zauna a gidan nan har zuwa muga abunda hali zaiyi dan kaina ya kulle.
“Wlhy badai gidan nan ba cewar Ummy.
Shima Abba a fusace yake magana, “idan gidan kine sai ki kore ta ai.
“Son kaje ka k’ara tinani akan zancen nan , na baka 2days.
Sultan bece komai ba ya mik’e yabar falon.
Abba da kansa yaje yasa masu aiki sumar gyaran wani 6angare a cikin gidn , Sultana zata zauna nadan lokaci.
Ummy tana shiga d’aki takira wayan Aminiyar ta akan tazo gida zancen bana waya bane , Hajiya Rahma Aminiyar Ummy ce sosai , tana bata shawara dana kirki dana tsiya duka , yanzun makan kullun ta bata sharan taringa bawa yarinyan aiki masu wuya zata bar gidan bbu wanda ya sani.
Zainab yau ma kaman kullun tana zaune da waya a hanun ta , ta had’a uban tagumi kiran duniya tayi Amma number din Mom din ta baya tafiya haka ma na Daddy, ta rasa Wanda zata bawa labarin abunda yake faruwa , dan komai na Mom din ta a boye sukeyi ko family d’in su basa bari susan cikin su, dan a cikin su kowa baya son ci gaban kowa.
Ayshwan ne ya fito daga d’aki , fiskan nan a tsume ya yiyo kanta “keh yaushe na fara wasa dake dan ubanki ?” .
“Me ya hana ki shan wannn maganin ?”, so kike ki tsufar dani?” , To wlhy baza ki haifu ba dole sai an zubar da cikin nan…
Zainab rinannun idanun ta ta d’aga tana duban sa tace” wlhy bazan zubar ba ai bana shege bane…
“Keh ina magana kina magana?”, Belt ya cire ya fara jiggarta kamar Allah ne ya aiko sa, sai da yayi ra ayi dan kansa ya barta .
Haka ta wuni da ciwon jiki, dare nayi kuma yazo neman sex , iya amfanin ta kenan a gunsa , daga sex sai duka.. …..Haka Zainab ta ci gaba da zama a gidan cikin k’uncin rayuwa , ta rame ta yi bak’i sai dai ta kasa gayawa kowa tabar abun a cikin ta , tunda Mom d’in ta bata kusa bare ta bata labarin abunda yake faruwa.+
Sultan ya koma gida duk hankalin sa a tashe ga 6acin rai , Zainabu ce ta ringa kwantar masa hankali har yaji zuciyar sa tamar sanyi a lokacin.
Kwana biyu Abban Sultan ya d’auka yana binciken lamarin amma ya kasa gano bakin zaren , sannan be’isa ya ce Sultana taje gidan iyayen ta ba domin a gabansa akayi komai uban ta yace shi da ita har abada , to yanzu kuma ga wannan matsalan.
Sultana ce kwance a cikin bargo sai faman rawan sanyi take yi , k’ara min yaro ne ya fad’o dakin bako sallama , yanda ya bankad’o k’ofan ne yasa Sultana d’aga kai dan ganin ko waye, Amir ta gani k’anin Sultan , du bansa take ba tare da tace komai bah har ya iso gaban ta.
Tsawa ya daka mata! , “keh dalla ni dai ki daina kallo na , tunda Ummy na bata son ki ni ma ba sonki zanyi bah .
Sultana baki mud’e take sake duban yaron , sai dai bata ce komai bah .
Amir harara ya watsa mata! sannan yace “dalla kizo , Ummy na neman ki.
Yana kaiwa nan ya fice a d’akin ba tare da yaji me zata cebah.
Sultana ba abunda take yi sai zubar da wasu hawaye masu zafi , ga tsananin ciwon da take ji, dak’er ta iya mik’ewa jiki na 6ari! ta fito ta nufi side d’in Ummy.
Sultana tayi sallama ya kai baki uku Amma ba wanda ya amsa bayan tana jin hayaniyan yara a cikin falon , ciki kuwa harda Ummy .
An d’au lokaci kafin aka amsa mata, falon ta shiga daga gefe ta samu waje ta raka6e, sai faman rawan sanyi take yi .
D’aya daga cikin yaran da ke falon ne ta fara magana , “ke kuma dalla sai wani faman 6ari kike yi , da uban waye yace kiyi cikin aikin banza marar tarbiya, mufida kenan k’anwar Sultan yarinyan bata da kunya .
Mufida juyawa tayi da duban ta gun Ummy , “ni kam Ummy ba nason ganin k’azaman nan sallame ta maza ta bar falon nan.
Ummy ne ta gintse fiska sannan ta fara magana , “wai me kike nufi ne?” da kikaje d’aki kika kwanta uban waye kika ajiye zai girka miki abincin?”ko kina da bawa ne?” , To bari kiji gaba d’aya masu aikin gidan nan nace suje gida su futa zuwa wani lokaci sai kin bar gidan sannan zasu dawo , yanzu kece me yi.
Duk maganan da Ummy take yi Sultana ba tace komai ba , kanta a sunkuye tana zubar da hawaye , sai kuma rawan jiki , Ummy taga hakan amma sai tayi kaman bata gani bah , saboda tsanan yarinyan ya riga ya shige tah .
Ummy ce ta dakawa Sultana tsawa! “Zaman meye kike yi agun ?” , Maza tashi kije kitchen ki fara aiki.
Sunsun Sultana ta mik’e zata bar falon , saidai Ummy ta tsaida ita , saida aka bi kan yaran duka ana tanbayan su kowa ya fad’i me zai ci.
Haka yaran suka ringa fad’a, girki kala biyar suka lissafa.
Sultana ji tayi zuciyan ta ya tsinke! , dan tasan yau akwai aikin indomie kawai ta iya dafawa , duk girkin da aka lissafa bata san yanda akeyi bah….
Fitowa tayi ta nufi kitchen d’in tana ta sak’e sak’e a ranta domin bata iya komai bah , ita yar gata ce a gidan su lallai wannan ake kira da *juyin rayuwa*, ta jima a kitchen d’in ta na tsaye saidai ganin tana bata lokaci yasa ta nufan wajen da gas yake , ashana ta d’auka ta kunna saidai take taji kanta na juyawa saboda warin gas din da bata Soo , hanci ta shiga toshewa amai ne yazo bakin ta da sauri ta fito a kitchen d’in , durk’ushewa tayi tana kwara amai sosai , ta ke duk jikin ta ya sake mik’ewa tayi zuwa gunda fanfo yake tana tafe tana had’a hanya saboda jiri da take ji , dak’er ta isa gaban fanfo ta wanke jikin ta.
Amir ne ya fito ya ga yanda Sultana tayi amai duk gaban kitchen ya 6aci , komawa yayi da gudu ya fadawa Ummy abunda ke faruwa saidai ko a jikin ta .
Saima cewa tayi “ai kad’an ta gani badai cikin shege ba , ai da saura wlhy ba taga komai ba amah.
Sultana takai 1hour agun tana zaune , Sam ta manta da tasa ruwa a wuta .
Ummy ce ta fito zata wuce , idon tane yaje gunda amai yake kwance duk da ya ma bushe dan uwane kawai tunda ba abunda Sultana take iya ci sai moltina , kuma tunda tazo gidan bata samu bah, k’udan da suke bin kan wajen ne yasa Ummy ganewa anan amai d’in yake , dan Ummy mace ce mai masifan tsafta , ba tason ganin k’azan ta ko a wani gun bare kuma a gidan tah.
“Ai ganin wannan amai d’in Ummy batasan lokacin da ta furta kan uba , toh wa ta barwa ya gyara mata?”.
Afusace ta nufi kitchen d’in saidai bbu kowa sai gas da yake kunne wuta nata faman ciii, ranta ya masifan 6aci fitowa tayi ta shiga d’akin Sultana saidai bbu kowa a ciki , ta fito zata wuce ta hango Sultana kwance a gun fanfoo, wajen ta k’arisa tana fad’a ” ke Wai me kike nufi ne?”.
Sultana a raza ne ta d’aga kai ta dubi Ummy , saidai ba tace komai .
Ummy ce ta sake daka mata tsawa “ba dake nake magana bah?”.
Da k’er Sultana ta iya magana “Ummy bazan iya ba bani da lafiya neh….Wannan k’arya ne , bana son zancen banza bazan d’au iskanci bah, dalla mik’e amai d’in da kika yi yana jiran ki , ko akwai bawan ki da zai kwashe miki amai d’an shege?”.+
Sultana dak’er ta iya d’aga Ido tana duban Ummy , k’ok’arin mik’ewa take yi amma ta kasa saboda yanda jiri yake d’iban ta.
Ummy ce ta sake daka mata tsawa , “zaki mik’e ne ko sai kinjin sauk’an mari?” , Ai wlhy wahala ta ganki tunda baki da zuciya , yaro yama sake ki amma kizo gidan su ki zauna , andai ji kunya an had’a da asara.
Sultana mik’ewa tayi tabar wajen tana zubar da hawaye, wajen aman da tayi ta nufa ta fara gyarawa , sannan ta wuce zata je d’aki ta kwanta.
Tsawan da Ummy ta sake doka mata ne ya sata saurin tsayawa, “keh ina zaki he?” , Uban wa zaiyi girki wato girkin ne baza kiyi ba shiysa ma kika kunna gas kika tafi kika barshi saboda mugun ta , ai inda ubanki ne yake refiling da baki barshi a kunne sama da 1hour bah, aikin banza.
Sultana baya ta dawo tazo gaban Ummy ta zube tana shar6an kuka,! “dan Allah Ummy kiyi hakuri wlhy idan na shiga amai zanyi…
“Amai zaki yi fa kike cemin?” , To me kike nufi?”.
“Ni na yarda zan muku girkin da ice, tayi maganan tana dafe kan ta saboda tsananin ciwon da yake mata kamar zai fashe.
“Shikenan Ummy ta furta a tak’aice, nanma ba tsananin tausayin Sultana bane yasa ta yarda , kawai dai gudun kar ‘a 6ata mata kitchen da amai ne yasa ta yarda.
“Shikenan za’a fito da murhu ki fara.
Hakan kuwa akayi , murhun aka fito dashi tare da ice , Sultana takai 1hour amma wutan yak’i kamawa da abun ya isheta sai ta fara kuka , saidai ganin bbu wani mafita yasa ta goge hawayen ta .
Wajen had’a girkin ansha daga , dan bbu abunda Sultana ta iya girkawa banda tea, indomie, acikin girki kala biyar da aka sata ko d’aya batayi ba dan bata masan taya zata fara bah .
Abunda yafi mata sauk’i ta za6a wato white rice and beans , shima sam bazai yiwu bah daga waken har shinkafan jik’a yayi bazai ciwu ba ko da wasa saboda wutan sam icen baya chi…
Duk yanda taso had’a source Amma ta kasa, attaruhu ta d’iba son rai ta sai gishiri maggin ma baji yayi bah , albasa kuma gaba d’aya bata sabah gashi da tazo yi duk ya k’one yayi bak’i , ni na tabbatar duk wanda yaci girkin nan yau zaiji a jikin sah😂😂😂.
STORY CONTINUES BELOW

Mommy Faty sosai take zuba iko yanzu , sai yanda tayi da Alhaji Musa yana mugun shakkan tah.
Yau dai Alhaji Musa ya tashi da matsanan cin ciwo , kasan cewan daman yana da suger , ba ko wani kalan abinchi yake ciba amma yanzu ko wani abinchi ci ya ke yi bbu yanda ya iya tunda shi Gimbiyar ta sa ta bashi , hakan yasa ciwon ya ringa cin jikin sa a hankali har zuwa yau da ya tashi da tsanani , bbu abunda yake yi sai wani irin nishi tun yana yi a hankali har ya koma yi da k’arfi , hakan ya ringa kira sunan ta , “Fatima Fatima ki taimaka min inajin yau mutuwa zanyi…
Momy Faty tana kwance a gadon tana jinsa taimakon ne kawai baza tayi bah, ido ta rufe! kamar me bacci , zuwa jimawa kiran da yake mata yasa ta bud’e ido! , tare da jan tsaki! a fili, sannan ta fara magana “magana ta gaskiya ka takura min kana shiga hakk’ina , haba Dan Allah wannan wani irin abune ?” , Ka zamo me hak’uri man, bazan iya ma komai cikin tsohon daren nan ba sai zuwa safe.
“Haba Fatima ki taimaka man , muje asibiti ni nasan me nake ji .
Momy Faty ba tace komai ta sake neman gu ta kwanta.
Zuwa anjima dai jin irin numfashin da ya ke yi yasa ta mik’ewa , d’aki ta shiga ta d’auko mayafi sai key din mota sannan ta dawo gunsa , da taimakon ta Alhaji Musa ya mik’e suka shiga Hospital , ambashi taimakon gaggawa har ya samu bacci , ita ma kwanciya tayi kasan cewa akwai gadon da mai jinya shima zai kwanta .
Washe gari da safe dctr ya kira Momy Faty office d’insa domin tattaunawa akan matsaln mijin nata , ance ciwon yaci jikin sa dole sai ammr aiki da gaggawa , idan ba hakan ba za a iya rasa shi , yanzu ana buk’atan kud’i a wajen 2.5 million , take ta amince zasu bayar sannan ta ranta6a hannu , ta kuma kar6i account number sannan ta fita.
Tana fita tayi dariyan mugun ta , “ai wlhy ko naira bazan bayar ba , saidai ya mutu.
Kai tsaye d’akin da yake kwance ta nufa , ta samun ciwon ya k’ara tashi sai faman 6ari yake jikin nan zafi kamar wuta , duk hakan be dametaba , magana ta fara yi cikin masifa”ka sakeni ka sauwak’e min bazan iya bah , ina buk’atar ci gaba da wani na mijin kasan jiki da jini sai a slow , yaushe rabon da ka biya min buk’ata na?”, so kake sha awa ta kashe ni ?” , Maza sake ni zan nemi lafiyayye me jini a jika, magana sosai ta ringa jefamar kallon ta kawai yake yi ba bakin magana sai da abun ya isheshi ne, dak’er ya bud’e baki yace na sake ki…
Dariya tasa! sannan tayi bucewar ta tana cewa toh saduwar alkairi sai wata rana.
Wasu hawaye ne masu zafi suka shiga gangaromar akan kuncin sa , yau shi Musa mace tayiwa haka?” saboda rashin Imani, kai ya dafe yama rasa me yake mr dad’i.
Ammasa aikin cikin sa’a saurn ya farka , annemi wacce take jinyan sa amna bbu , kud’i kuma bata sa musu a account bah.
Ko da ya farka aka shaida mar zancen kud’in da akamar aiki cewa yayi akwai a gida amma bbu anan, haka ma da aka tanbayi ina mai jinyan sa ya basu labarin yanda akayi be rage musu komai bah, Norse ne suka ci gaba da kula dashi kuma kullun yana k’ara sabon lafiya , ya tara bashin asibitin sosai a kanta, randa aka sallamesa aka had’asa da security akan suje gidan tare , beyi musu ba dan yasan akwai kud’in , saidai ko da suka je Sam bbu kud’i a gidan wayan sa ya shiga nema domin ya musu daga account din sa , amma ko da yaga wayan ba komai a ciki sai 200k , salati ya shiga yi tare da dafe kai yana cewa “shikenan ta kwace komai.
Cikin rashin fahintan zancen sa , security ke tanbayan sa “waye ?”
“Sannan me aka kwashe?”.
“Kud’i ta kwashe, ya fad’a yana dafe kai.
Babu mafita dole suka juya zuwa hospital din tare, ado kan k’asan dole sai an tsare Alhaji Musa kafin a nemi taimako agun mutane har a samu kud’in da hospital ke binsa bashi, hakan kuwa akayi wajen tsare masu laifi aka kaisa sannan aka ci gaba da neman taimako.
Momy Faty duniya ta samu , tabar India ta koma span da zama , akwai wani yaro da suke chart shima d’an Nigeria ne kuma yanzu soyayyy ne me k’arfi a tsakanin su auren sa takeson yi domin taci duniyan ta da tsinke, yanzu dai zuwan sa kawai take jira.
A6an garen Zainab tana mugun shan wahala hanun Ashwan , yanzu cikin ta ya shiga wata na hud’e , Ashwan ji ya keyi kamar ya kasheta dan bayason cikin , ya kuma hana kowa zuwa gidan ko da kazo daga get zaka juya domin kuwa mai ganin bazai bari ka shiga bah , Zainab sanin idan tabar gidan ma ina zata ne shiysa kawai ta hak’ura tasa idoo.
Zainab ceh kwance tana bacci , saidai kana ganin ta kasan baccin wahala ne , Ashwan ne ya shigo gidan kai tsaye falon ta ya shigo batanan kafin ya fita ya sata wanki da guga , kuma yanzu bega kayan bah , d’akin ta ya shiga kwance ya sameta tana bacci , “kan uba bacci ma kike yi?”.
Ashwan waya ya d”auko ya shiga zuba mata kamar Allah ne ya aiko sa , tun tana iya ihu har tayi shiru ga duk kan alama ta suma , ga kuma jini da yake bin ta.
Daga farko hakan bema dame Saba , sai daga baya yayi tinanin kar yayi kisan kai , juyawa yayi ya d’an dubeta kwance take kamar wani gawa , tsaki yaja sannan ya d’aga ta zuwa mota , suka nufi asibiti.
Hajiya Maryam ce ke zaune a cikin yaran ta da suka kawo mata ziyara suna ta faman tattaunawa akan matsaln da Sultana take fiskanta , uwa kenan duk abunda Sultana tayi mata ashe bata manta da ita ba , ashe tana sonta a hakan? , ta bartane kawai duniya ta koya mata hankali ba dan ta tsane tabah
Husna ce ta fara magana , “toh Momy kisa ta dawo gunki man tunda ya riga ya sake tah , meye amfanin taje gidan su ta zauna?”.
“Kayyah ke dai Husna ku bari tad’an yi hankali tasan duniya, duk da nasan ba laifin ta bane laifin mahaifin kune.
Ummul’kairi tace *Allah sarki ,ni dai tana ban tausayi wlhy duk da bata kyautawa uban nata me sonta bah .
“Yanzu dai ku kwantar da hankalin ku, komai ya kusan zuwa k’arshe zansan abunyi Nima inason Sultana zata dawo nan ba jimawa , ina bibiyan rayuwan ta a kullun ai nasan duk halin da take ciki.
Nasir yace “ni wlhy cikin jikin nata nafison ta haifa , shegiyar yarinya bata fara ban tausayi bah , kuma kuna ban mamaki , yarinyan da ta raba ku da uban ku , tasa kuma aka saki uwar ku , ai ta gama muku komai gashi ai ita d’in ma basa tare yanzu .
Husna tace “haba brother ka zama me yafiya mana.
Hmmm! , “ba zaki gane bane , yarinyan da tasa aka ki biya min kud’in karatu sai uwata ne ta biya , kud’i sai dai muga tana kashewa kamar mu bashi ya haifemu bah , abunda da cin rai.
Haka dai suna iringa tattaunawa a tsakanin su……..Acan asibiti kuwa Zainab ce kwance kaman gawa , dak’er doctors suka yi nasarar ceto ranta , tasha wuya sosai Safna k’anwar Ashwan ita ke jinyan Zainab , dan duk cikin dangin Zainab bbu wanda yazo asibitin mahaifiyar Ashwan kullun tana zuwa duba ta , Zainab ko da wasa bata yi gigin sanar da iyayen Ashwan abunda ya faru ba dan tana mugun tsoron sa , haka shima Ashwan ce musu yayi wai fad’uwa tayi saidai duk mai hankali yasa ba hakan bane tunda duk jikin tah shatin duka ne .+
Kwanan ta hud’u aka sallamesa daga asibitin , ta dawo gida , abar mata Safna akan ta tayata zama zuwa wani lokaci dan daman Ashwan zaiyi tafiya ya dai cewa iyayen nasa zaije k’aro ilimi ne agun aikin sa an tura sa wani course .
Ita kam Zainab taji dad’in hakan sosai zata futa nadan lokaci, murna ta shiga yi sosai dan har abun ya bawa Safna mamaki tayi magana ,”haba Aunty Zainab mijin ki zaiyi tafiya amma sai murna kike yi , ni dai idan nayi aure mijina zaiga kula zaiga tarairaya dasoo ba wlhy.
Dariyan kafin kuka ciwo Zainab tayi , tare da wayen cewa ta sanja zancen zuwa wani hiran daban .
Washe gari Ashwan yabar k’asan .
Ita ma Sultana a nata 6angaren bayan ta gama had’a komai da ya shafi girkin da tayi , kai tsaye daining table ta kai ta jere su , sannan ta kama gaban ta tunda daman baci takeyi bah .
Saidai matar gidan da yaran gidan suka fito cin abinci ne suka fara kallon kallo , dan a kullun ana musu girki ababu kala uku kowa ya ci wanda ya ke so , amma yau kula kala d’aya ne bbu k’ari.
Amir ne ya bangaji Mufida , “ni kam batsa min yunwa nake ji nawa aka gama sauran naku.
Mufida hanu ta d’aga za ta kai masa duka! , da sauri ya matsa yana sosa k’eya ta da cewa “haba Aunty ni ne fa.
K’wafa tayi tare da jan zaki , ta ce “to sai meye ?”.
Amir ya ce “sai kiyi hak’uri nake nufi ai.
Hmm! kawai ta ce suka k’arisa gaban table d’in.
Ummy kam tinin daman taje gun ta bud’e flast dan ganewa idon ta ko me aka girka , abun da ta gani yasa ta yin shiru kamar me tinanin wani Abu.
Bayan isowan su Amir ne tayi magana , ” ni fa bnga food d’in bah , anya wannan yarinyan tana da hankali?” , Ko ni sa’arta ne?”.
Da sauri Mufy ta ce “Ummy me ya faru?”.
“Meye kuwa idan banda wannan shegiyar yarinyan , abunda tayi takai k’arshen maganan tana nuna kulan abinci.
Mufida bud’ewa tayi dan ganin meye a ciki , a fili ta furta “kan ubannan wannan girkin ta mana amma ta raina mana wayoo.
Ummy ta ce “kai Amir maza je ka kira min ita kaji ko.
“To ya amsa , sannan ya ruga da gudu ya nufi 6angaren da take.
Ba’a d’au lokaci ba suka shigo tare .
“Gani Ummy tayi maganan tana dafe kanta wanda yake ciwo kamar zai fad’i.
Harara Ummy ta watsa mata sannan ta ce “ina girkin?”.
“Shi ne wannan Sultana tayi magana cikin k’arfin hali .
“Abunda na saki kenan?”, Ummy ta jefa mata tanbaya.
“A’a kiyi hakuri dan Allah , Ummy wlhy shima dak’er na yi shi , take k’arshen maganan tana mai rushewa da kuka!….
Ummy taso tayi masifa sosai amma kawai sai taji tausayin yarinyan yazo mata , shiru tayi bata sake cewa komai bah.
Sultana taci gaba da tsayuwa agun , sai da Mufy ta daka mata tsawa sannan ta fice a d’akin ta kama gaban tah.
Mufy tsaki taja! , Sannan ta bud’e food d’in ta fara d’i ba , dan mugun yunwa take ji , haka shima amir.
Ai kuwa loman farko abinci ya kasa had’iyuwa Mufida sai amai , shima Amir zubar da na bakin sa yayi sannan ya ringa wanke bakin.
“Tab lallai matsaln babbane Ummy ta furta a fili cikin 6acin rai , abincin ta d’and’ana ai kuwa da sauri ta zubar agun .
Waya ta ciro ta Kira masu aikin da tace suje gida dan ta gane ba abunda Sultana ta iya.
A ranan da kanta ta shiga kitchen ta had’a musu abinci , washe gari yan aikin gidan suka dawo , yanzu ta sake juya aikin Sultana shara da wanke wanke wankin band’aki , sharan d’akunan gidan .
Sultana tana mugun Shan wuya saidai bbu yanda ta iya dole tayi , ta rame tayi bak’i duk ta fita a haiyacin ta idan ba wanda ya santa sosai ba bazai gane taba , cikin yana mugun bata wuya ba komai take iya ciba kuma bbu wanda zai bata abunda take so a gidan saidai ta saya da kud’in ta , toh yanzu duk yan kud’in ma sun k’are hatta wayan hanunta ta siyar bata da wani madogara a yanzu , kullun tana cikin kuka wai yau ita Sultana na ce ta dawo hakan ?” , Lallai wannan shi ake kira da *Juyin Rayuwa*, anya mahaifin ta bashi ne ya zalunceta bah , tanbaya da yawa take yiwa kanta amma bbu amsa dole tayi shiru, aiki kuma basai anyi magana ba tun asuba take farawa ba yanda ta iya , lallai dangi suna da amfani a yau inda ta sansu da taje gunsu Amma bata sansu ba.
Abu kaman wasa cikin ta sai k’ara girma yake yi , Abban Sultan baya kula da yanda duk ta sanja kala a tinanin sa cikin ne yake bata wuya , kuma duk ganin da zai mata da himar a jikin ta , kuma har cikin ransa ya d’auka Ummy na bawa Sultana kulawa , dan shi tunda yaga bata sake mar zancen ba sai kawai yace ta saki ranta ne zuwa suga me Allah zaiyi besan ba hakan bane……….Yau dai Sultana ta tashi bata jin dad’in jikin ta , hakan yasa bata fito tayi aikin da ta saba yi bah kullun, har Ummy ta fito falo duk da falon bbu wani datti a cikin sa amma bin falon Ummy ta ringa yi da kallo kamar ta fahinci ba a shareba duk da cewa bbu dattin kawai dai kullun tana sa turare da ta gama gyarawa yau kuma bata sabah.
Tsakan gidan tad’an fita saidai ganin bbu Sultana yasa ta kiran Larai mai aiki.
“Larai ina wannan yarinyan take ne ?”.
Larai baki ta saki dan bata gane zancen bah .
“Ina magana kinsa ido kina kallona , Sultana nake nufi .
“Uw Hajiya aida ban fahinci zancen bane , inaga tana d’aki yau bata fito bah.
“Ohk kimin kiran tah.
Da sauri! Larai ta nufi 6angaren da Sultana take ta shaida mata Ummy na kira, Sultana ido ta d’aga tana duban Larai ita d’aya tasan abunda take ji a jikin tah , “pls Inna Larai ko zaki min sharan nasan akan sane kiran wlhy banda lpy ne.
Ita ma Larai cikin tsananin tausayawa ta dubi Sultana “ki daure kije kinsan halin Ummy bata da dad’i , idan ta shiga d’aki zan miki yanzu kije Kiran.
Sultana bata musa bah ta mik’e tana bin gini har ta fice daga d’akin .
Daga gefe Sultana ta tsaya tana yamutsa fiska alaman ciwo , wani mugun kallo Ummy ta watsa mata sannan tayi magana, “sai wani raku 6ewa kike kamar wata munafuka ko dake ai daman muna fukar ce tunda kinsan yanda ake d’ibo cikin shege macucita keda d’a na sai dai hange daga nesa..
“Yau kuma wa kika barwa aikin yayi ko kina da bawa a gidan nan?”.
” Cikin 6arin jiki Sultana ta fara magana kiyi hak’uri Ummy wlhy na tashi banda lpy shiysa kika jini shiru .
“Toh uwar yan iya magana , kiyi maza ki kama aiki Dan wlhy bbu sassauci tsakanina dake idan kin gama kizo ina neman ki.
Sumu sumu Sultana ta wuce wajen aikin kamar yanda ta saba , tadau lokaci kafin ta gama kasan cewan yau bata da lpy, bayan ta gama ta zo gun Ummy tunda tace tana neman tah.
Firan doya Ummy ta sata Wai yau Sakwara suke son ci, bbu musu Sultana ta fice zuwa kitchen , ta fere ta wanke ta had’a wuta ta dora , saidai k’irjinta duka kawai yake yi dan bata jin zata iya dakawa, gashi lokacin Larai taje kasuwa bare ta taya ta , haka ta fito da turmi tahau daka duk da ba wani k’arfine da ita bah.
Tana yi tana goge gumi kantane ya fara juyawa saboda azaba , duhu ta fara gani kawai sai ta zube agun .
Tad’au lokaci kafin Larai ta shigo gidan , Larai kamar wanda aka ce duba can Sultana ta gani a zube bbu alaman numfashi , cikin tsananin kad’uwa ta iso wajen “Uwar d’aki nah , Uwar d’akina , innalillahi me yake faruwa ?” , ganin tanbayan kanta ba shine mafita ba yasa ta kwasa da gudu zuwa falon Ummy.
Daga nesa ta fara “Ummy Unmy , gacan Sultana kwance bbu rai .
Ummy zuciyar ta tayi mummunan tsinkewa amma saita dake kamar bata damuba .
“Keh Larai ba nason shiririta , wannan wani irin magana ne?”.
“Wlhy ga ta can kwance , ranga ranga .
Ummy mik’ewa tayi suka fito tare zuwa wajen , yana yin da Ummy taga Sultana ya matuk’ar bata tsoro , jikin ta har 6ari yake!.
“Keh Larai yi mazo ki k’ira IDi driver yazo muje asibiti.
Cikin sauri Larai ta nufi hanyan fita zuwa kiran driver.
Ummy cikin ta har 6ari ! Yake yi sai ayau ta fara dana sanin abunda ta yiwa yarinyan nan , sharrin zuciya da kuma zuga irinna muguwar k’awa.
Sunje asibitin doctors biyar ne suka taru akan Sultana suna k’ok’arin ceto rayuwar ta , saidai suka d’au tsawon lokacin sannan suka yi nasarar yin hakan.
Ummy ce zaune a bakin d’akin da Sultana take ta zubar uban taguma danasani da nadaman abun da ta yi sune suka cunkuse mata , ta rasa ina zata sa kanta yanzu idan yarinyan nan ta muku ya zama tayi kisan kai kenan ?” , anya K’awarta aminiyar ta ta mata adalci wajen bata shawara kuwa ?” Anya son Allah take mata ?” Abunda tayiwa Sultana Anya Allah zai barka?” , Tabbas ta cuci yarinyan nan dan itace silan faruwan komai da taimakon gurguwar shawara irinta Aminiyar tah , to wai meye ribar su Sune silar canzawa Sultan zuciya ba ciwo ne yayi tsanani bah🤦🏻♀🤦🏻♀🤦🏻♀🤦🏻♀.Nan fa allura ta tono garma, sirrin da suka rufe yau ya bud’u lallai son zuciya bashi da wani rana ko ribah, lokacin da aka kai Sultan asibiti bayan Ummy taji abunda ya faru har Sultan ya fad’i taji bak’in ciki bana wasa ba , sannan taji tsanan Sultana sama da komai acewarta Sultana ita ce ta 6ata Sultan saboda abunda idon ta ya gani tun had’uwar su a airport, hakan yasa ta kasa zaune da tsaye shine ta kira k’awar ta Aminiyar ta wato Hajiya Kubra akan ta nema musu mafita dan sun jima da son had’a yaran nasu aure wato Sultan da fauziya y’ar gidan Hajiya Kubra , shi Sultan bema san yarinyan ba itace dai take haukan sonsa, Uwar ta kuma kullun tana cikin bin malamai dan ganin cikar burin su, bawai burin Hajita Kubra ta taimakawa Ummy ba itama cikar burin d’iyar ta kawai take fata, shiysa tanajin zance a hotel aka kamasu da waccer yarinyan tayi alwashin ko ta yaya saita raba su kawai , Dan haka ta kawo shawara ita kuma Ummy ta kar6i shawara da hanu biyu….+
Nan suka fara tinanin zuciyar waye za a sanjawa Sultan basu taba tinanin sanja zuciya zai shafi cikar muradin suba , a tinanin su idan an sanja shikenan duk wani son da Sultan ya kewa Sultana ya k’are ashe ba haka bane hausawa sukace wasa farin girki.
Kud’i mai yawa aka bawa dctr kafin ya amince da k’udinsu , sannan yace musu baza a samu matsala bah.
Lokacin da Ahmad saurayin zainabu yazo birni kana ganin sa kaga rashin wayewa kasan bak’o ne , kwanan sa biyu a garin kaduna ranan yahau titi da nufin zallakawa kawai aka bugesa Wanda ya bugesa ya dagashi zuwa mota suka wuce asibitin , Ahmad ba mutuwa yayi ba sanjin zuciya kawai aka mar sannan yanzu haka yana rayu baya dai k’asar ne yana wani wajen dabn a kar’k’ashin kulawar su Ummy allura akamar a wancan lokacin sai yayi dogon suma , alokacin da Sultan ya farka da tinanin Ahmad nason Zainabu hankalin Ummy yayi bala’in tashi dan har tace anemo Ahmad ya dawo asake sanja zuciya , amma sai dctr yace baza ayi hakan ba abari a hankali komai zai dawo normal.
Hajiya kubra taji haushin wannan lamarin amma bbu yanda ta iya dole , dole tasa ido saidai tana ta faman shiga malamai a kullun amma har yanzu ba a dace bah.
Mufida tana jin duk sanbatun da Mahaifiyar ta keyi , itama tashiga rud’u da tashin hankali , ana cikin hakan taji fad’uwan mutun juyawan da zata yi sai ganin Ummy tayi a zube a k’asa.
Wani k’ara tasa cikin sauri ta fara Kiran sunan Ummy amma shiru , da sauri tashiga takira doctor yazo Ummy bata san inda kanta yake ba ahaka aka shigar da ita d’akin taimako gaggawa , jinin tane yahau sosai.
Mufida waya ta d’auka tama rasa waye zata kira , Big Brother din ta tafara kira amma shiru ba a d’auka bah yakai 10 miscalls amma shiru , bbu ynda mufy ta iya dole ta kashe wayan ta ajiye, can kuma ta sake d’auka ta rasa waye zata Kira dan bata son kiran Abba tunda baya gari kar hankalin sa ya tashi , gashi wayan Ummy yana gida dole ta hak’ura ta zubawa saurautan Allah idoo.
Gado suka bawa itama Ummy dan jinin tane yahau sosai har ana tinanin ko tasamu matsaln shanyewan 6arin jiki .
Mufida ce agun mahaifiyarta , Larai agun Sultana duk ma tana bacci kuma bazata tashi da wuri ba dan anmata alluran bacci , shiysa ita ma Larai baccin tayi cikin dare ihun Sultana ya farkar da ita tana da wayyoo cikin ta zata mutu hankalin larai ya tashi sosai duk da ta nemo likita amma tana nan tana zubar kwalla , idan haka ta yanke hukuncin sanar da mahaifiyar Sultana halin da ake ciki tunda daman duk wani labarin Sultana Mamy tana samu ne agun Larai dan har kudi take biyan ta sunsan duk halinda Sultana ke ciki .
Sultana haka ta ringa juyi har a suba , anan ne kuma cikin jikin ta ya zube , ba a 6ata lokaci ba aka mata wankin ciki kawai danta futa gaba d’aya .
Asubar fari Mamy tazo asibitin gun d’iyar ta , ta shiga damuwa da yanda taga d’iyar tata , Allah ya sani tana son Sultana Amma mijin ta Alhaji Musa shine silan komai tabbas kar uwa taga ana fifita mutun daya acikin yaranta taji dadi dan ba abun farin ciki bane a raba maka kan yarah, yanzu duba yanda rayuwar yarinyan nan ta zama , bayan ya bata ta sannan ya guje tah.
Gari na waye wa takira sauran yaran ta suka hallara a hospital d’in, lokaci Sultana na bacci duk bata San abunda akeyi bah sai bayan da ta farka taji dadi sosai tanemi yafiyar su ta zubar da hawaye ba Kad’an bah lallai Dan uwa duk yanda yake akwai dadi .
Bayan farkawan Ummy abunda ta fara yi shine neman doctor din da ya yiwa su Ahmed canjin zuciya , ya kuma zo ta bada umarnin a dawo da Ahmed , da farko dctr din yaso yak’i saboda gudun fitowan maganar nan fili Amma ganin ta rikice masa yasa shi yrda Ahmed zai dawo, saidai sun makara domin wani dctr ya jisu.
Sultan anashi bangaren ashe yana gida bashi da lafiya duk ya birkice kuma yace bazai je hospital ba sannan baza a sanar da iyayen sa bah, Zainabu ido ta sa mar dan bayn da zata yi da shi.
Saida yaga bbu sarki sai Allah ya amince suje hospital d’in , suna zuwa kuwa aka rik’esa , Ummy an sallame ta koda taje gun Sultana Mamy cewa tayi tabar d’akin basa buk’ar ta ta kama gaban ta haka dai Ummy tabr d’akin jiki ba karfi.
Wani ciwon kai ne me tsanani yake damun Sultan ashe zuciyar sane duk abunda ya manta yanzu suke dawowa, dadai alluran bacci ake mar saboda ya samu futu zuciyarsa ta futa , yaran ya farka da safe Zainabu ce a gefen sa yana bud’e ido ita ya fara gani sai binta da kallo yake da sauri ta taso zuwa gabansa tana mar sannu Amma kamar ke da bakya wajen , dama abun ya ishe shi sai ya daka mata tsawa! “Keh wace irin maiya ne ki barni banason ganin ki ha a , ina Sultana ?” Ita nakeson gani ki nemo min ita….Zainabu ranta yayi bali’in 6aci , ji tayi wani abu ya tokare mata wuya , d’ikin ta bari ta nemi waje ta zauna a waje cikin jin zafin abunda ya mata , a ranta tace “to sai meye aikin banza ai daman bance dole sai ka zauna da niba kaje ka nemeta man Allah yasa kullun shawara mai kyau nake baka akan matar ka banta6a jin komai akan taba wlhy tausayin tama nake ji .+
Sultana kam kwanan ta uku aka sallame tah ,Mamy ta d’au yarinyan ta suka wuce gida.
******
Ashwan tunda ya sa k’afa ya bar k’asan bbu wani labari dan ko iyayen sa baya kira , su kuma kullun idan suka kira shi a kashe sai randa yaga daman kira sannan zai kira su idan sunyi k’orafi yace inda yake ne bbu ntwrk dole suyi shiru , ita kam Zainab hakan ma bata samu saidai bata wani damu ba dan hankalin ta yama fi kwanciya , dan har d’an k’iba tayi duk tana da matsala amma dai tana ganin dotr kuma anasarn zata zamu sauk’i , tun lokacin da Ashwan ya mata dukan kawo wuk’a bayan ta dawo gida sai bata iya rik’e fitsari dataji zai zubo maran ya sake saidai ance abari zuwa ta haifu ko matsalan ciki ne , abudai idan aka ce bbu uwar ka a kusa shine kawai amma ai wannan babbn matsala neh , idan akwai mai kula da kai a kusa.
*******
Span Momy Faty ne akan wani makeken gado sai wani matashin saurayi Wanda ta kishin gid’a tayi matashin kai da ciyar sa , yana ta mata wasa da gashin kanta tana k’ak’arin bacci sai faman lushe ido take yi , ga duk kan alama maganan da suke yi ne bemata dadi ba , d’ago kai tayi tana dubansa tana zuba shagwa6e sai faman rarrashinta yake yana riritata.
Take itama ta fara mayar masa martani , lokaci daya suka tafi wata duniyar ta dabn saida wannan yaron ya gama futawa da jikinta sai wani nishi take yi tare da kuka k’asa k’asa juyawa tayi ta cire goga daga rijiya🤦🏻♀ sannan ta juya ta koma itane a saman sa ta haye kan faffad’an k’irjin sa ta rungumo sa gaba daya tare da ja musu bargo su rufu sosai .
Ni kuma wannn lamari ya d’aure min kai dan haka na kujera na zauna ina ganin ikon Allah, har suka yi bacci suka tashi ina gun…..👌🏼👌🏼
Bayan sun tashi tare suka yi wanka suka fito manne da juna sai faman tarairaya take sha .
Saida suka shirya sannan ya sake duban ta , tare da cewa ” ki fahince ni zuwa gidan na dole ne zan dawo nan bada jimawa ba , kuma ina dawowa zamu yi aure kinji ko.
STORY CONTINUES BELOW

Had’a fiska Momy Faty tayi “ni fa banason kaje Nigeria ka barni anan gaskiya mu zauna kawai nikm, kodai akwai abunda na rageka dashi neh?”.
“Noo wlhy komai kina min , ni kaina zanyi missing , idan na tafi dawa zan futa?” .
“Atoh badai ka dage sai kaje bah ai ga hanya , Amma zan shiga damuwa idan ka tafi.
Shima langabar da kai yayi a jikin ta kamar zaiyi kuka , “sorry baby duk muna cikin damuwa amma Daddy na ya nason ganina dole naje zan dawo ai , shima yakai k’arshen maganan kaman zaiyi kuka!😢
Momy Faty bata son ganin damuwa a fiskan masoyin nata cikin sauri ta sake jiwosa jikin ta , tare da manna masa breast d’inta a baki bbu musu ya kama ya fara sha yana lunshe ido , hanunsa ya sa a k’asan ta dan gyara kwanciya tayi yan da zai samu ya sake , sun jima a haka kafin suka mik’e zuwa gun cin abinci.
Ashwan wanda ya sanja suna da Sahir , tinin ya gane ciki gare ta shiysa yake son ya gudu dan duk yan matan sa dasun yi ciki yake rabuwa dasu.
Washe gari yabar k’asar cike da kewar ta , duk da bewani damu ba saidai yasan yayi missing kulawa agunta.
*****
Bayan fitowan Alhaji Musa daga gidan yari sai ya koma gararanba a titi bashi da komai , wataran Babban Dan Nura yaje India kawai ya hadu da Mahaifin nasa yana bara a titi dan lokacin bashi da komai , Nura ya kad’u da wannan lamari rayuwa kenan yaran da ya zubar ya mayar marasa gata gashi yanzu sune zasu dawo gatan sah, Nura ne ya kaishi masauk’in sa bayan ya gama abunda zaiyi suka dawo Nigeria a tare, ya hada shi da sauran yaran sa kuma ya nemi yafiyar su duk sun yafe mar , da taimakon yaran sa ya dawo da matan sa duka , sun kuma hadamar wani sabon jari yaci gaba da kasuwa.
Sultan tun yana Asibitin ya saki Zainabu saki d’aya, tabbas taji tashin hankali a wannan ranan , amma bbu yanda ta iya dole tanemi hanyan gidan su, danma zuwa lokacin tana da yan kud’in ta cikin account dan kullun yana cikin zuba mata bata kashewa, yanzu sa mata amfani .
Shikan wancan doctor din da yaji abunda su Ummy da Ogan su na hospital gaba d’aya suka aikata report yayi ba tare da sun san ya sani bah, saidai aka d’auko Ahmad sannan officer’s din suka zo suka tattara su aka wuce dasu station domin wannan ba k’aramin abu bane suka aika tah.
Su Hajiya Kubra ido ya raina fata , sai da akaje har k’auyen yarima aka taho da iyayen Ahmad , sunma sunga abun mamaki ashe daman be mutu bah?” , daman anayin hakan?” , Kafin kace meye wannan ai zancen duk ya cika garin , case akayi sosai anbawa Ahmad kudi masu yawa ya je dasu gida , dan yace abar zancen ya yafe , saidai duk da hakan an kar6i kud’i masu yawa ahanun su Ummy tare da tsare su a gidan kaso na kimanin wata uku…
Zainabu kam gani take kaman bbu wanda ya fita farin ciki da faruwan lamarin, dan haka tana gama idda ba a dau lokaci ba aka d’aura musu aure.
Sultan ya koma neman auren Sultana saidai iyayen suka ce baza su bashi ba, Sultana bata wani damu ba , Sultan ya shiga damuwa yanzu ya k’ara hankali yanda ya ringa naci ne yasa aka bashi auren Sultana.
Bayan dawowan Ashwan da 2month Zainab ta haifu , Ashwan be wani nuna farin ciki ba sai ma bakin ciki k’arara akan fiskan sah , lokacin suna ba a wani yi hidima ba dan Zainab bbu lafiya tunda ta haifu take fama da matsalan yoyon fitsari ga kuma hawan jini dan taji labarin dawowan Alhaji Musa Nigeria har gidan sa taje saidai ya mata korar kare tare da bata labarin abunda mahaifiyar ta ta masa , ita kanta Zainab bata ji dadin hakan bah shiysa ta dawo gidan mijin ta , take kuma hak’uri da di da rashin dadi, su kansu iyayen Ashwan yanzu ba sonta suke yi ba tunda suka samu labarin abunda mahaifiyar ta tayi.
Momy Faty tana ta zaman jiran dawowan Ashwan wanda ta sanshi da Sahir , amma shiru bbu labari ga number dinsa baya tafiya gashi kuma duk wani kud’i nata yana hanunsa dan ta bashi akan zasu hada suyi business , ga k’ana nan ciwuka da take fama dashi ta rasa gane kanta kimanin 5months kenan ga rashin kud’i duk abun duniya ya dame ta , yau dai ta yanke hukuncin zuwa asibiti ko zata samu maganin matsalar ta , dan ynzu abunda take ji yayi yawa ga wani Abu da yake yawo a cikin ta , ako tana zuwa asibiti gwaji farko aka samu tana d’auke da ciki har yayi wayo dan ya shiga wata na shida, Sam tace banda cika kam dan ko batan wata bata yi bah , saida akayi scanning aka nuna mata baby kwance a mahaifar ta sannan ta yarda tabbs ta shiga tashin hankali bad’an Kad’an ba , tane mi da acire cikin zata biya ko nawa ne amma akace ai cikin ya wuce zubarwa danko ta ma kusan haifuwa , abir kice tabar asibitin ta wuce gida goal ta d’auka takai kasuwa siyarwa dan shine kawai ya rage kayan kud’i a hanun tah , tanemi viza tako yi dace ta samu , washe gari ta nufi Nigeria , rasa ma ina zata fara sauk’a tayi sai kawai ta wuce gidan k’awar ta , Zuwairat ta kar6e ta hanu biyu dan a tinanin ta har yanzu akwai kud’in banza a hanun Momy Faty , sai da dare take bata labarin abunda yake faruwa ai kuwa Zuwairat ta d’aure fiska tace saidai Hajiya Faty ta kama haya zaman su tare bazai yiwu bah, Momy Faty bata wani damu ba , dan daman tasan hakan zai iya faruwa .
STORY CONTINUES BELOW

Washe gari tunda safe ta shirya ta shiga gari neman Sahir amma bbu labari wuni guda sannan ta dawo dan bata ma bi takan d’iyar ta Zainab bah, nandai ta tina tanada address din wani abokin sa da sukayi waya a gaban ta hankalin ta yad’an kwanta , washe gari ta fita neman wancan abokin ta koci sa a an dace , saidai shi besan wani Sahir bah saida ta gaji da kwantance sannan dabara ta fado mata akan ai sai ta nuna picture dinsa , wayan ta ta ciro ta bud’e gallary ta nuna pic d’in Ashwan wanda take ta Kira da Sahir, daria Abdul yayi!, ” Uw Ashwan ne kike nema?”.
Cikin rashin fahinta Momy Faty ta ce “Ashwan kuma?”.
“Eh sunan sa kenan.
Shiru tayi nadan lokaci sannan tace “eh shi nake nema yanzu ina zan ganshi?”.
“Eh toh saidai na baki number dinsa , ko kinfison kwatancen gidan sa?” .
“Eh inasoo , amma number d’in ma zaiyi amfani duka kaban .
“Ohk…
Kwatancen gidan ya mata , duk yasan matsala ne hakan amma daman sunyi fad’a yana neman ta inda zai rama sai gashi Allah ya kawo sanadi har gida, number din ya kuma bata sannan sukayi sallama tayi godia ta wuce.
Kai tsaye gidan taje bata sha wani wahala ba wajen ganewa , a waje ta tsaya ta Kira wayan sa dan ita ama tinanin ta gidan iyayen sa ne , tunda shi bashi da aure.
Saida tayi 3miscalls , sannan aka d’auka.
“Hello aka furta daga bangare d’aya , ka fita ina jiran ka a waje….
Ashwan San begane muryar ba , d’an tsaki yaja sannan ya fito wajen gidan..
Dam! zuciyar sa ta buga saboda ganin me neman sa , dak’er ya iya d’aga k’afa ya k’iriso gun, zuciyar sa cike da tnbayoyi dabn dabn shin ina ta samu address dinsa mah?”…
Wani mugun Kallo Momy Faty ta watsawa Ashwan “baka yi tinanin ganina bako ?”, bakin munafuki macuci to Allah ya Toni asirin kah…
Ashwan yana magana k’asa k’asa amma ita momy Faty tinin ta d’aga murya .
Jin hayaniya ne yasa Zainab lek’owa ta window,ako rass ras gabanta ya fad’i dan ganin da babar ta mijin ta ke fad’a.
Da sauri ta fito wajen tana raba ido , idan ganin abun take kamar a mafarki.
“Umma ke ce nake gani a gabana?”.
Dam! K’irjin Momy Faty ya buga ganin d’iyar ta a inda bata yi zato bah, gashi yarinyan duk ta jeme ta sanja kala , baki rama bbu abunda kake gani sai ido .
“Nice baby , maza taho nayi kewar ki…
“What what , me kuke nufi ne?” .
Zainab dake kukan farin ciki ta dubi Ashwan tace ” me muwa muke nufi ni da mahaifiya ta…
“Mahaifar ki?”.
“Eh akwai matsala ne?”
Shiru yayi ita kan momy Faty zubewa tayi agun tana wayyo tashiga uku kenan cikin sirikin tane a jikin tah?”.
Kamar a mafarki Zainab taji fitan zancen “Umma me kika ce?”, Ciki na waye ?” .
Hajiya Fatima bata sake motsi ba agun saboda tashin hankali , asibiti aka kaita domin ceto rayuwar ta.
Ashwan be ta6a na daman neman matan banza ba sai a yau, ina wannan babbar magana ne ai dole iyayen sa suji, bbu yanda ya iya dole ya ciro wayansa ya danna Kiran Daddyn sa ya shaida masa akwai matsala suna asibiti, ba a dau lokaci ba suka zo wajen , nanfa ya shiga bada labarin abunda yake faruwa duk kansu sun kadu dajin labarin , har madai Zainab da tazama mutun mutumi.
Momyn sakan cewa tayi ya saki yar ma a take , hakan ko akayi ya dannawa Zainab saki dan sunce had’a zuriya dasu ma bala’i ne.
Cikin k’ankanin lokaci zancen ya baza gari har asibitin ake zuwa Kallon su dan sunyi abun kunya, Alhaji Musa ya samu labari shima yazo ganin k’arshen me son zuciya , ya kuma nemi kud’in sa nan ta shaida masa duka kud’in suna hanun Ashwan , annemi Ashwan an samu wasu wasu kuma bbu su , ya krbi Wanda suka samun, rayuwa kenan duk abunda zakayi kayi shi tsakani da Allah saboda gaba bakasan me zata haifar bah, lokacin da kud’in jinyn su ya k’are bbu yanda suka iya dole suka bar hospital basu da ko inda zasu zauna gidan da Momy Faty ta gada duk ya lalace bbu yanda yake cikin sa suka koma da rayuwa , abunda zasu ci basu dashi sai Zainab taje gidan da take yin wanke wanke da girki sannan ta samo musu , ahaka har Hajiya Fatima ta haifu, Zainab ce ta shaida wa Ashwan haifuwan amma ko zuwa beyi bah….
Yanzu Ashwan ya zama mutumin kirki sosai har zuwa d’aukan karatu take yi wajen malamai ya daina duk abunda yake yi ynzu , Auwal d Muhammad tare suka taso aka sasu makaranta duk tare sun rungumi yaran bbu yanda suka iya , bayan shekara goma sannan Ashwan ya nemi inda suke yakai musu ziyara lokacin girma yazo ya musu alkairi ya kuma nemi da a bashi yaran su dawo gunsa da zama bbu musu suka bashi , Zainab ta auri wani me mata uku ita ta hunu tayi hak’uri ta zauna hakah.
Sultana da Sultan yaran su uku , suna zamn lafiya sai wanda ya gani , dagin mijin nan kamar zasu cinye Sultana dan soo , ita da Sultan sun zama kamar wasu taurari basa ganin girmn su a kullun suna mugun bawa junan su kulawa suna damuwa da damuwan junan su….
Itama Zainabu yaran ta 4ynzu suna zama ne a Abuja , saboda mijin ta yanzu babban d’an kasuwa ne wnda akeji dashi a Nigerian kuna bawa mutanen k’auyen su taimako ta fanni dabn dabn , kamr irinsu makaranci ruwansha kai duk wani kayan more rayuwa sun samu ci gaba sanadin su Zainabu da Ahmad suna Shan albarka a kullun….
Alhamdulillah!
Alhamdulillah!!
Alhamdulillah!!!
Anan na kawo k’arshen wannan labari